Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai A Tabbatar Da "Tsayi" Ba Ne Har Ma Da "Zafi"
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

byCGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Sauye-sauyen da ake gani a wani lungu na wani birni ya kan iya nuna ci gaban da daukacin wata kasa ta samu. 

Misali, a yau na raka wani abokina dan Najeriya zuwa ofishin hukumar shige da fice ta birnin Beijing na kasar Sin, domin kula da wasu harkoki, sai na tarar da yadda hukumar ta kaura zuwa wani sabon gini da aka kammala, mai taken “Cibiyar Hidimomin Gwamnati”. A wurin, ana iya kammala ayyukan da suka shafi hidimomi na gwamnati nau’ika sama da 1,900 cikin sauri, ta hanyar nemo tagar da ta dace, da aka kebe wa masu bukatar daidaita mabambantan harkoki. Wato yanzu babu bukatar yin kai-komo tsakanin hukumomi daban-daban, kamar yadda a kan yi a wasu lokuta a baya.

  • Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
  • Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Bari in yi muku karin haske kan taken wannan bayani: “Tsayi” na nufin manyan gine-gine da suke nuna yanayin ci gaba na wani birni, da habakar tattalin arzikinsa. Kana “zafi” a nan ba ya nufin yanayi, maimakon haka yana nufin jin dadi da gamsuwar mutanen da ke zaune a cikin birnin. Kula da wadannan bangarori guda biyu yadda ya kamata, shi ne umarnin da gwamnatin kasar Sin ta gabatar wa jami’ai masu kula da birane 694 na kasar.

A yau da ni da abokina mun gama ayyukanmu cikin sauri, mun fito daga Cibiyar Hidimomin Gwamnati, sa’an nan mun waiwayi baya, mun ga cikakken tsarin wannan babban gini mai salon zamani. Abun da muke ji shi ne: Beijing ta samu karin ci gaba. A lokacin, mun shaida “tsayi” na ci gaban birnin Beijing, da kuma “zafi” na birnin a cikin zukatanmu.

Wani taro da ya gudana a baya-bayan nan game da aikin raya birane a kasar Sin, ya ta’allaka ne kan manufar “amfani da tsare-tsaren birane wajen samar da hidimomi ga jama’a”, tare da ba da shawarar raya biranen kasar, don su zama masu sabbin fasahohin da aka kirkira, da ingancin muhallin rayuwa, da kyan gani, da iya tinkarar bala’i, da wayewar kai, gami da basira. Alal hakika, tun tuni an riga an fara aiwatar da wadannan ra’ayoyi a biranen Sin: Tun daga shekarar 2019 har zuwa yanzu, kasar Sin ta kammala aikin gyaran tsoffin ungwanni kusan 280,000, da kafa na’urorin lif sama da 130,000, da gina karin wuraren ajiye motoci miliyan 3.8, da sabbin filayen motsa jiki da fadinsu ya kai murabba’in mita miliyan 31.

Har ila yau, Sinawa sun yada irin wannan ra’ayi na raya birane don bautawa jama’a, zuwa nahiyar Afirka . Misali, a Lagos na Najeriya, layin dogo na “Blue Line” da wani kamfanin kasar Sin ya gina ya takaita lokacin zirga-zirgar jama’a da dama, daga minti 90 zuwa minti 20. Kana a birnin Lusaka na kasar Zambia, tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa da wani kamfanin Sin ya gina, ta sa an samu karin hasken fitilu, a shaguna daban daban dake kan titunan birnin a cikin dare.

Ban da haka, a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha, aikin kwaskwarima da kamfanonin kasar Sin suka gudanar, sun mayar da wani kango cike da laka zuwa daya daga cikin filayen wasa mafi girma da inganci da ake samu a cikin biranen Afirka.

“Ya kamata a tabbatar da ‘tsayi’, gami da ‘zafi’, yayin da ake raya wani birni.” Bari mu tuna da wannan magana ta shugaban kasar Sin Xi Jinping, mu kuma shaida yadda sannu a hankali ta zama gaskiya a birane daban daban na kasar Sin da na kasashen Afirka. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version