Manyan Makarantun Bauchi Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makarantun Bauchi Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani

byKhalid Idris Doya
9 months ago
Makarantu

Kwamitin haɗakar (JAC) na ƙungiyar malamai da waɗanda ba malamai ba na manyan makarantu mallakin gwamnatin jihar Bauchi sun shelanta tafiya yajin aikin sai babaa ta gani wanda hakan zai kai ga kulle makarantu baki ɗaya bisa rashin aiwatar musu da sabon tsarin biyan albashi na dukkanin ma’aikatan manyan makarantu wato (CONPCASS da CONTEDISS).

Shugaban kwamitin JAC, Kwamared Abubakar Ahmed wanda ya karanta jawabin bayan taron gaggawa da suka gudanar a ofishin ASUP da ke kwalejin ATAP ranar Litinin, ya ce, yajin aikin zai kai har a kulle makarantun dukka zai fara ne daga ranar Alhamis 2 ga watan Janairun 2025.

  • NDLEA Ta Kama Mutum 415, Ta Kwace Tan 1.2 Na Kwayoyi A Bauchi
  • Kirsimeti: ‘Yansanda Sun Kama Mutane 15 Da Ake Zargi Da Laifin Sata A Bauchi

A cewarsa, sun ɗauki wannan matsayar ne biyo bayan rashin gamsuwa da irin amsar da suka samu daga wakilan gwamnatin jihar da kuma irin nuna rashin damuwa da suka yi da buƙatun ƙungiyar a yayin zaman sulhu da suka yi a tare.

Kwamared Abubakar ya ce sun kuma cimma matsayar ne bayan ƙarewar wa’adin mako biyu da suka bayar wa gwamanti na yajin aikin gargaɗi da suka yi daga ranar 16 zuwa 30 na watan Disamban 2024 ba tare da samun wani sakamakon mai kyau daga wakilan gwamnati ba.

Makarantu

Makarantun da suke ƙarƙashin JAC ɗin sun haɗa da kwalejin kimiyya da fasaha ta Abubakar Tatari Ali Polytechnic, Bauchi da kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa, Kangere da Kwalejin ilimi da nazarin ilimin Shari’a da karatun komai da ruwanka ta A.D Rufai da ke Misau da kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke Azare da kwalejin ilimin harkokin noma da ke Bauchi da kwalejin horas da nasu da ungomaza ta Bill and Melinda Gates da ke Ningi.

Kwamitin ya nuna damuwarsa kan yadda wakilan da gwamnatin ta turo suke ƙoƙarin kawo naƙasu ga azamar gwamnan jihar na kyautata harkokin ilimi a manyan makarantun jihar, inda suka nemi a gaggauta aiwatar da sabon tsarin albashi kamar yadda yake ƙunshe a tsarin CONPCASS da CONTEDISS.

Injiniya Abubakar Ahmed ya nuna damuwa kan yadda ake barazana ga jagororin JAC da mambobinsu a faɗin makarantun bisa yadda suke tsayuwar daka wajen ganin an biya musu buƙatunsu. Sai ya nemi iyaye da dalibai da su yi haƙuri da zarar komai ya daidaita za su koma bakin aikinsu yadda ya kamata.

Makarantu

Kana sun yi kira ga gwamnatin jihar Bauchi Bala Muhammad da ya tashi tsaye ya bibiyi lamarin domin gudun janyo naƙasu ga harkokin ilimi da kuma nazartar matakan da wakilan gwamnati ke ɗauka wanda ƙungiyar ta ce sam ba za su taimaka ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version