Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Kwamitin hadaka na manyan makaratun guda biyar da ke jihar Bauchi (JAC), sun ayyana tafiya yajin aikin jan kunne na tsawon kwanaki 14 da zai fara aiki daga ranar Laraba 19 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 30 ga watan Yulin 2022 domin jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta share musu hawayensu.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a wani taron da suka kira, Shugaban JAC, Abdulkadir Mohammed, ya ce bukatun da suke da su, sun kunshi a gaggauta biyan albashin dukkanin mambobin kungiyar ke bi ba tare da bata wani lokaci ba.

  • 2023: Muna Fata APC Ta Dawo Mulki A Jihar Bauchi -Kwamared Sabo

Wakilinmu ya nakalto cewa hadakar makaratun sun hada da Kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa da ke Kangere da Kwalejin ilimi, koyar da ilimin shari’a da sashin ilimin komai da ruwanka ta A.D Rufa’i da ke Misau da Kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke garin Azare da Kwalejin Ilimi da  Koyon aikin gona ta jihar Bauchi da kuma babbar Kwalejin Kimiyya, fasaha da kere-kere mallakin gwamantin jihar Bauchi, ATAP.

Kazalika, kwamitin ya yi kira da a gaggauta dawo da aiwatar da tsarin karin girma na shekara-shekara ga wadanda suka dace da aka dakatar da yi ba tare da an bayyana a hukumance dalilin dakatarwar ba tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau kan mulki.

Shugaban kungiyar ya ce kwamitin nasu ya nuna adawarsa kan shigar da ma’aikata tsarin taimakekeniya ta fansho duk kuwa da cewa hatta ma’aikatan Gwamnatin tarayya ma na kaurace wa tsarin domin wahalar da ke janyo wa ma’aikatan.

A cewarsa, su na kuma da bukatar a dauki dukkanin matakan da suka dace wajen samar wa mambobin kungiyar rayuwa mai inganci da kuma tsaron hakkokinsu a kowani lokaci domin samun dama da sararin gudanar da aiki ba tare da wani fargaba ko dar-dar ba.

Abdulkadir Mohammed ya ce sun kuma yi adawa da cire wani kaso daga cikin albashin ma’aikatan da sunan shirin tallafin gidauniyar kiwon lafiya da ake kira BASHMA.

Mohammed ya ce bisa wadannan dalilai da sauran hakkokinsu da suke nema ne ya sanya suka zauna suka cimma matsayar tafiya yajin aikin gargadi, kodayake kafin wannan ya ce sun bai wa gwamantin wa’adi da jawo hankalinta tun da jimawa amma matsalolin nasu sai karuwa suke yi. Don haka ne suka ga dacewar tafiya yajin aikin.

Ya cigaba da cewa domin neman adalci dai, sun tuntubi hukumomin da abun ya shafa kan matsalolin nasu domin ganin an yi shawo kan kalubalen da suka hada da Akanta Janar na jihar, da kwamishinan ilimi, da sauran masu ruwa da tsaki kan lamarin amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da tilin wasikun da suka aike musu.

“Mun rubuta wasika muka aike wa mai girma gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad Abdulkadir a tunanin mu duk abun da suke faruwa bai ma san da su ba. Nan ma dai ba mu samu sauyi ko canji daga matsalolinmu ba.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Bauchi

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version