Isah Ahmed">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Marubutan Kafofin Sada Zumunta Sun Bukaci Al’ummar Najeriya Su Yada Zaman Lafiya

by Isah Ahmed
January 6, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Marubutan Kafofin Sada Zumunta
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kungiyar marubuta a kafafen sada zumunta ta ‘Arewa Media Writers’ ta bukaci al’ummar Najeriya, su kasance masu yada zaman lafiya, da kaunar juna da zamantakewa, a rubuce rubucen da suke yi a kafofin sada zumunta, na zamani. Shugaban kungiyar reshen Jihar Filato, Malam Abba Abubakar Yakubu ne, ya bayyana wannan bukata, a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida, bayan kammala babban taron shekara, da kungiyar ta gudanar a garin Jos, a karshen makon da ya gabata.

Har ila yau, ya shawarci marubuta su rika amfani da kafofin sada zumunta, wajen fahimtar da al’umma kan mahimman abubuwan da suke faruwa, tare da zaburar da shugabanni kan aikata mahimman abubuwan da suka kamata, ba zagi ko cin mutunci ba.

samndaads

Malam Abba ya yi bayanin cewa an kafa wannan kungiya ce, da manufar hada kan marubutan Arewa karkashin inuwa daya, don yin magana da murya guda, ta hanyar amfani da kafafen sada zumunta na zamani. Don a samar wa Arewa ci gaba, da mafita daga kalubale da take fuskanta.

Su ma da suke nasu bayanan, wasu daga cikin ‘yayan kungiyar, Abdulhadi Abdullahi Cokali da Mu’awuya Mai Dankali Jos da Hajara Muhammad, sun jaddada muhimmancin amfani da kafafen sada zumunta, wajen kawo sauyi mai amfani a cikin al’umma. Don haka, sun bukaci marubutan Arewa su hada kai, wajen samar wa Arewa mafita kan matsalolin da take fuskanta, ta hanyar amfani da kafafen sadarwar zamani.

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Shugaban Karamar Hukumar Lokoja Ya Rantsar Da Sabbin ’Yan Majalisar Zartarwarsa

Next Post

Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafin Kayan Miliyan N100 A Asibitoci

RelatedPosts

Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Boko Haram A Borno 

by Isah Ahmed
7 hours ago
0

Rundunar sojan Najeriya ta bayyana samun nasarar tarwatsa sansanin da...

Jam'iyyar Adawa

Jam’iyyar Adawa Ta PDP Ta Yi Babban Kamu A Kebbi

by Isah Ahmed
7 hours ago
0

Jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kebbi tayi babban kamu...

Majalisar Malamai

Majalisar Malamai A Kogi Ta Raba Zakkar Miliyan N2.5 Ga Mutum 63

by Isah Ahmed
7 hours ago
0

Majalisar Malamai ta Najeriya,reshen jihar Kogi(Council of Ulama) ta rarraba...

Next Post
Dan Majalisa

Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafin Kayan Miliyan N100 A Asibitoci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version