Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masarautar Katsina Ta Warware Rawanin Hakimin Bakori, Makaman Katsina

Dama An Dakatar Da Shi A Watan 11 Na Shekarar 2022

byEl-Zaharadeen Umar
3 years ago
Katsina

Masarautar Katsina ƙarƙashin jagorancin mai martaba sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ta warware rawanin makaman Katsina, Hakimin Bakori daga sarauta.

Hakan yana kunshe ne a cikin wata sanarwar da Kauran Katsina, Hakimin Rimi Alhaji Aminu Nuhu Abdulkadir ya sanyawa hannu a madadin masarautar Katsina sannan aka raba wa manema labarai a Katsina.

 

  • 2023: Manyan ‘Yan Takara Na Shafa Wa Juna Kashin Kaji

Sanarwar ta ci gaba da cewa ta warware rawanin makaman Katsina, Alhaji Idris Sule Idris ne bisa wasu korafe-korafe da masarautar ta samu inda ta gudanar da bincike kafin yanke wannan hukunci.

A cewar fadar mai martaba sarkin Katsina, kafin ɗaukar wannan mataki sai da majalisar sarkin Katsina ta samu wata takarda daga ofishin sakataren gwamnatin jihar mai lamba SEC/54/VOL.VI/1416 da ta amince da cewa bincike ya tabbatar da samu tsohon makaman Katsinan da laifin da ake zargin sa da aikatawa.

“Haka kuma binciken da masarauta ta gudanar ya nuna cewa duk wasu zarge-zarge da ake yi a kan tsohon makaman yana da masaniya akan su” wanda a cewar fadar sarki hakan na iya haifar da rashin zaman lafiya a yankin Bakori” in ji sanarwar.

Daga ƙarshe dai masarautar ta Katsina ta yanke shawarar sallamar makaman Katsina hakimin Bakori daga sarauta a jiya alhamis 19/1/2023, sannan ta yi fatan Allah ya ba da zaman lafiya.

Idan za a iya tuna masarautar ta Katsina ta dakatar da makaman Katsina hakimin Bakori Alhaji Idris Sule Idris a ranar laraba 23/11/2022 bisa wasu zarge-zarge da masautar ta ce an gabatar a gaban ta sai dai ba ta yi ƙarin haske a kan korafe-korafe ba har zuwa yanzu da aka kareshi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Mutum Miliyan 20 Na Fuskantar Hatsarin Cutar Koda A Kasar Nan – Shugabar NAN

Mutum Miliyan 20 Na Fuskantar Hatsarin Cutar Koda A Kasar Nan - Shugabar NAN

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version