Ahmed Mu'd Danasabe">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Masu Garkuwa Sun Nemi Diyyar Miliyan N25 Kan Tsohon Shugaban Karamar Hukuma A Kogi

by Ahmed Mu'd Danasabe
December 21, 2020
in LABARAI
2 min read
Shugaban Karamar Hukuma
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu satar jama’a ne sun yi garkuwa da tsohon shugaban karamar hukumar Olamaboro dake jihar Kogi, Barista Emmanuel Isaac Ekpa a yankin Ochadamu da ke karamar hukumar Ofu da ke jihar.

Irin wannan lamari ya auku a makon jiya, inda wasu yan bindiga suka yi awon gaba da mai rikon mukamin Sarkin Ankpa dake jihar ta Kogi,( Ejeh) Alhaji Shaibu Usman a ya yin da yake kan hanyarsa ta zuwa masallaci don yin sallar Asuba.

samndaads

Masu garkuwa da mutanen sun samu nasarar sace Sarkin na Ankpa mai daraja ta daya ne da misalin karfe 5.30 na safe gab da fara sallar ta Asuba a ranan juma’a wadda a wannan rana ce masu garkuwa da mutanen suka saci tsohon shugaban karamar hukumar Olamaboro a yankin Ochadamu dake karamar hukumar Ofu akan hanyarsa ta zuwa garinsu,kamar yadda wakilin jaridar LEADERSHIP Ayau ya nakalto.

An ce Ekpa yana shirye-shiryen bikin binne mahaifinsa ne kafin wannan ifti’lai ta fada kansa.

Wakilin LEADERSHIP Ayau ya tuntubi kakakin rundunar yan sandar jihar Kogi, Mista Williams Ayah, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin,yana mai cewa tawagar yan sanda dake yankin Ofu sun gano wata mota da babu kowa a cikntai a kan hanyar Ochadamu.

Ya ce bayan sun yi bincike cikin motar ne,sai suka gano ID card mai dauke da sunan Emmanuel Isaac Ekpa, alamun dake nuna cewa lallai yan bindiga sun yi garkuwa da shi.

Kakakin rundunar ya ce a yanzu haka, kwamishinan yan sansan jihar Kogi, CP Ayuba Edeh ya umurci rundunar yan sanda dasu shiga faraurar masu garkuwa da mutanen tare da tabbatar da ganin sun kubutar da Barista Emmanuel Isaac Ekpa.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Bullo Da Shirin Noman IFAD Ne Don Zamanantarwa – Musa Malumfashi

Next Post

’Yan Bindaga Sun Yi Garkuwa Da Sarkin Ankpa A Jihar Kogi

RelatedPosts

Gwamnan Bauchi Ya Amince Da Murabus Din Sakatarenshi

Gwamnan Bauchi Ya Amince Da Murabus Din Sakatarenshi

by Ahmed Mu'd Danasabe
2 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad...

Fitaccen Dan Jarida A Duniya, Larry King, Ya Rasu

Fitaccen Dan Jarida A Duniya, Larry King, Ya Rasu

by Ahmed Mu'd Danasabe
8 hours ago
0

Fitaccen mai watsa shirye-shiryen talabijin da rediyo, Larry King, wanda...

EFCC Ta Cafke ‘Yan Damfarar Intanet 11 A Osogbo

EFCC Ta Cafke ‘Yan Damfarar Intanet 11 A Osogbo

by Ahmed Mu'd Danasabe
9 hours ago
0

EFCC ta cafke wasu mutane 11 da ake zargi da...

Next Post
Sarkin Ankpa

’Yan Bindaga Sun Yi Garkuwa Da Sarkin Ankpa A Jihar Kogi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version