Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Masu Hakar Ma’adanai 138 Ke Neman Bashin Naira Biliyan 14.6

by Yusuf Shuaibu
December 3, 2020
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Masu Hakar Ma’adanai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Yawan wadanda suka bukaci bashin hakar ma’adanai na gwamnatin tarayya a fadin kasar nan na naira biliyan 14.6 sun kai guda 138. A ranar Talata ce, aka bayyana cewa, wadanda suke bukatar amsar wannan bashi na naira biliyan 14.6, wanda bashi ne da asusun hakar ma’adanar na biliyan biyar yake bai wa masu hakar ma’adanai, wanda aka samar a shekarar 2017 karkashin ma’aikatar masana’antu da kasuwanci da zuba jari tare da hadin gwiwar bankin masana’antu. An dai karkasu bashin ne zuwa kashi biyu, inda na farko za a bayar da na biliyan 2.5, sannan kashi na biyun ma zai kasance biliyan biyu wanda jamilla ya kama naira biliyan biyar.

Ministan hakar ma’adanai da bunkasa karafa, Olamilekan Adegbite shi ya bayyana hakan a wajen taron karawa juna sani wanda ya gudana a Abuja, domin mayar da hankalin yadda za a tallafa wa kananan kungiyar masu hakar ma’adanai. Haka kuma, Adegbite ya bayyana cewa, ma’aikatarsa ta yi wa sama da kananan kungiyoyi hakar ma’adanai rijista guda 1,495 tare da cibiyoyi masu sayan ma’adanan guda 368.

samndaads

Ya ce, “a cikin kananan kugiyoyin hakar ma’adanai guda 1,495 da aka yi wa rijista, guda 140 ne kungiyoyin zinari. Yankin Arewa maso Yamma ne suka fi yawan kungiyoyin da aka yi wa rijista, yayin da Kodu masu Yamma ke da kaso dan kadan.”

Ministan ya kara da cewa, “a ranar 30 ga watan Satumbar shekarar 2020, an sami yawan masu neman bashin hakar ma’adanai na naira biliyan 14.59 guda 138, inda ake ta kara amsar wasu daga baya.

Adegbite ya ci gaba da bayyana cewa, wannan rarraba kudaden ya yi karanci idan aka kwatanta shi da yawan mutanen da suke bukatar amsar kudaden, saboda sai masu nema sun cika wadansu sharudda na bankuna kafin a sami nasarar ba su kudaden. Ya kara da cewa, gwamnati tana aiki tukuru domin tabbatar da ganin cewa, an samu saurin rarraba kudaden.

SendShareTweetShare
Previous Post

Za A Fara Shirin Gwamnati Na Saka Lantarkin Hasken Rana Miliyan Biyar

Next Post

Ba Zan Sayar Da Rigar Maradona Ba, Cewar Steve Hodge

RelatedPosts

Lantarki

Bangaren Lantarki Ya Tafka Asarar Naira Biliyan 20.5 Saboda Karancin Gas

by Yusuf Shuaibu
20 hours ago
0

Bangaren wutar lantarki a Nijeriya ya tafka asarar harajin naira...

Matsalolin

Masana Sun Bayyana Hanyoyin Da Nijeriya Za Ta Bi Wajen Dakile Matsalolin Tattalin Arziki

by Yusuf Shuaibu
20 hours ago
0

Masana harkokin kudade da na tattalin arziki sun bukaci gwamnati...

Tattalin arziki

Yadda Ta’addanci Ya Lakume Tattalin Arzikin Dala Miliyan 80 A Arewa – Buhari

by Yusuf Shuaibu
20 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta...

Next Post
Steve Hodge

Ba Zan Sayar Da Rigar Maradona Ba, Cewar Steve Hodge

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version