Masu Sana'ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sana’ar Bola-jari Sun Buƙaci Gwamnatin Nijeriya Ta Tallafa Musu Da Rancen Kuɗaɗe

byMuhammad
2 years ago
Bola-jari

Kungiyar dillalan masu sana’ar Bola-jari ta Nijeriya ta kasa, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta ba su lamuni mai sauki domin fadada harkokin kasuwancinsu.

Dillalan na jari-bola sun kuma bukaci gwamnati da ta yi duba kan hukumomin tsaro da su daina muzgunawa mambobinsu.

  • Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja
  • Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

Shugaban shugabannin kungiyar, Alhaji Aminu Hassan, ne ya yi wannan roko a taron masu ruwa da tsaki na kungiyar a ranar Lahadi a Abuja.

Kungiyar ta masu sana’ar Bola-jari, kungiya ce da take da rijista a hukumance a karkashin dokar kungiyar kwadago, Cap. T14, na dokokin Tarayyar Nijeriya 2004.

Ita ce jigo ta duk mutanen da ke sana’ar Bola-jari, kuma take rarrabawa kamfanoni masu sarrafa lallatattun kaya su juya su zuwa sababbi kaya.

Masana sun ce sana’ar tana samun sama da Naira tiriliyan daya a duk shekara.

A cewar Hassan, kungiyar na matukar bukatar kudade da kariya domin bunkasa gudummawar da take bayarwa ga tattalin arzikin kasa.

“Muna da mambobi har miliyan biyar, amma suna aiki a cikin yanayi mai wahala,” in ji shi.

Hassan ya yi zargin cewa jami’an tsaro na cin zarafinsu “musamman wajen isar da kayayyakinmu ga kamfanonin da ke hakar man fetur”.

“Saboda haka, muna kira ga gwamnatin tarayya da ta shiga tsakani ta kuma taimaka mana wajen bin diddigin wannan mugunyar dabi’ar domin ba mu damar gudanar da harkokinmu ba tare da wata matsala ba.

“A jihar Kano kadai muna da mambobi kusan miliyan guda da suke bazuwa a fadin jihar ba a maganar jihar Legas inda muke da mambobi kusan miliyan biyu a sana’ar Bola-jari.

Shugaban ya kara da cewa “Kasuwancin da ke da dimbin mambobi sun cancanci tallafin kudi da kariya daga gwamnatin tarayya don ba su damar yin aiki yadda ya kamata.”

Hassan ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sa baki kan farashin kayayyakin da suke sayar da su, kar a bar wa kamfanonin da suke kasuwanci da su.

“Wadannan kamfanoni, galibin kamfanonin kasashen waje, mallakar Sinawa da Indiyawa, suna sha’awar canza farashin kayayyakin da suke saya daga gare mu yadda suke so, wani lokacin ba tare da sanar da mu, masu kawo kayayyaki ba.

“Wannan ci gaban ya shafi kasuwancinmu sosai.

“Misali, za ku iya siyan kaya a kan Naira 500,000, amma idan kun isa kamfanin, za su ce muku ba za su iya siyan sa fiye da N400,000 ba.

“Wannan yakan haifar da babban rashi ko asara daga bangarenmu. Ka yi tunani bayan ka sayi samfur akan N500,000 kawai ka gama sai ka siyar da shi akan N400,000.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

Wakiliyar Musamman Ta Shugaban Kasar Sin Ta Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version