Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Mata Ke Kawo Mana Abinci – Wadanda Suka Kubuta A Delta

by
2 years ago
in JAKAR MAGORI
2 min read
abinci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Mahdi M. Muhammad

 

Mutane 11 da aka sace wadanda aka saki a daren Talata sun bayyana cewa, mata su na kawo mu su abinci sau biyu a kowace rana a inda aka yi garkuwa da su na tsawon mako guda.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Shark Ya Hadiye Mai Ninkaya Tsawon Dakika 30 Kafin Ya Amayo Shi

Kotu Ta Tsare Mutum Shida Bisa Laifin Kisan Kai

An yi garkuwa da su mako guda da ya gabata a kan hanyar karamar hukumar Ekrerabbwen Ughelli da ke Arewacin titin gabas ta yamma na hanyar Warri da ke Jihar Delta, inda wasu da a ke zargin ‘yan daba ne su ka kama su.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Onome Onobwakpoyeya, ya tabbatar da sakin nasu.

Daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da shi wanda ya yi magana a Warri, a karkashin sharadin sakaya sunansa ya bayyana cewa, wadanda suka yi garkuwar da su a wannan ranar bai nuna cewa suna harin wani ba. Sun zo kan hanya ne da yammacin ranar don yin garkuwa da mutane koma su wanene. Sun kuma bude wuta kan motoci, kuma motocin da suka tsayar da mutanen an yi garkuwa da su,” in ji shi.

Da yake ci gaba da bayyana faruwar lamarin, wanda ya kubutar ya ce, mako guda da suka yi a hannun masu satar mutanen sun buge su don ganin sun kira abokai da dangi don neman kudin fansa na sakin su. Wasu daga cikin dangin wadanda aka sace sun iya biyan kusan naira dubu dari biyar don sakinsu.

A cewar wanda aka azabtar, an yi garkuwa da su kusan mutane ashirin da wannan yamma, ya kara da cewa, sai suka kasa su kashi biyu zuwa sansanoni daban-daban.

“Masu satar ba su da wasa ko kadan. Abin da kawai suke so shi ne kudi. Suna da mata wadanda ke kawo mana abinci sau biyu a rana. A cikin duka mutanen da suka sata sun samu kudi mai yawa a matsayin kudin fansa kafin a sake mu,” in ji shi.

Wadanda aka saki din sun bayyana cewa, an rufe musu idanu kuma an bi da su ta cikin koguna zuwa inda aka sare su na tsawon mako guda. A can masu satar mutanen za a gansu sanye da abin rufe fuska kuma suna dauke da muggan makamai.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Manajan Banki Da Wasu Matafiya 15 Da Aka Sace Sun Kubuta

Next Post

Muhammadu Sambo Wali Gidadawa (Bagimbane): Gwarzonmu Na Mako (1)

Labarai Masu Nasaba

Shark

Yadda Shark Ya Hadiye Mai Ninkaya Tsawon Dakika 30 Kafin Ya Amayo Shi

by
8 months ago
0

...

Kotu

Kotu Ta Tsare Mutum Shida Bisa Laifin Kisan Kai

by
9 months ago
0

...

Gwamnan Jihar Adamawa

An Daure Wani Dan Kasuwa Saboda Cin Mutuncin Gwamnan Jihar Adamawa

by
9 months ago
0

...

EFCC

EFCC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Damfarar Naira Miliyan 425 Ta Intanet A Gaban Kotu

by
9 months ago
0

...

Next Post
Sambo

Muhammadu Sambo Wali Gidadawa (Bagimbane): Gwarzonmu Na Mako (1)

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: