Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Matasa Sun Kwato Shanunsu Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Katsina

by
2 years ago
in JAKAR MAGORI
2 min read
Masu Garkuwa Da Sarkin Ikulu Sun Nemi Fansar Milyan 100
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Jama’a mazauna kauyen Sabon Garin Nasarawa da ke Karamar Hukumar Danmusa ta Jihar Katsina sun zama jajirtattu, kamar yadda jaridar Katsina Post ta wallafa. Jama’ar sun tattara duk wata jarumtarsu tare da yin gaba-gaba da wasu ‘yan bindigar daji wadanda suka kai musu hari a sa’o’in farko. Kamar yadda rahotanni daga Katsina Post suka bayyana, ‘yan bindigar masu tarin yawa a kan babura sun tsinkayi kauyen wurin karfe 12:30 na rana.

Sun yi awon gaba da dabbobinsu, kayan abinci da abubuwa masu muhimmanci na jama’ar kauyen. Amma kuma bayan da ‘yan bindigar suka sakankance cewa sun yi nasara, matasan sun yi jarumta inda suka zagaye gonaki tare da dazuzzukan da ke kusa.

Rahotanni sun bayyana cewa, matasan sun yi nasarar kashe daya daga cikin ‘yan bindigar tare da kwato dabbobinsu da suka sace. Amma kuma, a wannan karon, ‘yan bindigar sun kashe daya daga cikin mazauna kauyen tare da raunata wani, wanda a halin yanzu ya ke gadon asbiti inda a ke kula da shi.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Shark Ya Hadiye Mai Ninkaya Tsawon Dakika 30 Kafin Ya Amayo Shi

Kotu Ta Tsare Mutum Shida Bisa Laifin Kisan Kai

A wani labari na daban, dakarun rundunar Operation Sahel Sanity sun kashe ‘yan bindiga biyu, sun damke 12 daga ciki tare da ceto wasu jama’a masu yawa da aka yi garkuwa da su a jihohin Katsina da Zamfara a makon da ya gabata. Wannan na kunshe ne a wata takardar da mukaddashin Daraktan yada labarai na hukumar tsaro, Birgediya Janar Benard Onyeuko ya fitar a ranar Litinin. Onyeuko ya ce, “A ranar 28 ga watan Augustan 2020, dakarun sojin Nijeriya da ke Maru sun kai wa wasu da ake zargin ‘yan bindiga samame yayin da suke kokarin shiga kauye Gobirawa. “Cike da kwarewar dakarun tare da taimakon ‘yan sa kai, sun hana ‘yan bindigar shiga kauyen.

“Yayin samamen, dakarun sun yi musayar wuta da ‘yan bindigar inda suka kashe biyu daga ciki, amma wasu sun tsere da miyagun raunika. An ga jini a kasa wanda ya bayyana hanyar da suka bi.”

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Biyu Sun Mutu, Dan Sanda Ya Bata A Rikicin ’Yan Ci-ranin Anambara

Next Post

Mun Shirya Bin Dokokin Bude Kasuwannin Jihar Kaduna –Sarkin Kasuwar Zariya Kewaye

Labarai Masu Nasaba

Shark

Yadda Shark Ya Hadiye Mai Ninkaya Tsawon Dakika 30 Kafin Ya Amayo Shi

by
8 months ago
0

...

Kotu

Kotu Ta Tsare Mutum Shida Bisa Laifin Kisan Kai

by
9 months ago
0

...

Gwamnan Jihar Adamawa

An Daure Wani Dan Kasuwa Saboda Cin Mutuncin Gwamnan Jihar Adamawa

by
9 months ago
0

...

EFCC

EFCC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Damfarar Naira Miliyan 425 Ta Intanet A Gaban Kotu

by
9 months ago
0

...

Next Post
Mun Shirya Bin Dokokin Bude Kasuwannin Jihar Kaduna –Sarkin Kasuwar Zariya Kewaye

Mun Shirya Bin Dokokin Bude Kasuwannin Jihar Kaduna –Sarkin Kasuwar Zariya Kewaye

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: