Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Matsalar Tsaro Da Korona: Alarammomi Sun Yi Saukar Alkur’ani 313 A Wudil

by Abdullahi Muhammad Sheka
January 1, 2021
in LABARAI
1 min read
Alarammomi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A ci gaba da kokarin da ake yi na gudanar da addu’o’i, domin neman saukin matsalar tsaro da kuma Annobar Korona da ta kara dawowa, Majalisar Mahaddata Alkur’ani Reshen Karamar Hukumar Wudil, karkashin Shugaban Majalisar Gwani  Yakubu Hashim, sun shirya taron addu’o’i, kamar yadda Shugaban Majalisar Mahaddatan Alkur’anin na Kasa, Gwani Aliyu Saluhu Turaki ya bayar da umarni ga daukacin Alarammomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44.

 

samndaads

Taron addu’ar da aka gudanar a ranar Alhamis da ta gabata, a Babban Masallacin Juma’a na Garin Wudil, inda aka gayyaci Alarammomi 313 suka gudanar da saukar Alkur’ani 313 domin neman taimakon Allah da ya yaye mana matsalar tsaron da ke barazana ga ci gaban kasa baki-daya da kuma rokon Allah Ya dakile Annobar Korona, wadda a halin yanzu ta sake dawowa a karo na biyu.

 

 

Shi ma a nasa jawabin, Hakimin Wudil wanda Dagacin cikin garin Wudil Alhaji Mohd  ya wakilta, ya jinjinawa kokarin Alarammomi bisa wannan gagarumar gudunmawa wadda ya ce ita ce kadai mafita ga matsanancin halin da al’umma ke fama da shi, saboda haka sai ya bukaci al’umma su kara himmatuwa domin gudanar da irin wadannan addu’o’i.

 

Alarammomi daga daukacin mazabu goma na Karamar Hukumar ta Wudil ne suka halarci taron addu’ar da kuma sauran wadanda aka gayyata duk sun halarci taron addu’ar.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kasafin 2021 Ya Tabbata Yayin Da Shugaban Kasa Ya Rattaba Hannu

Next Post

KAROTA Ta Cafke Inyamurin Da Ya Yi Safarar Tabar Wiwi Katon 60 A Kano

RelatedPosts

Sheik Karibullah

Sheik Karibullah Ya Nada Alhaji Kabiru Sani Kwangila Khadimul Nabiyya A Taron Maulidin Gidansa

by Abdullahi Muhammad Sheka
28 mins ago
0

A ranar Lahadi ne aka gudanar da Maulidin Manzon Allah...

Magance Matsalar Tsaro

In Dai PDP Na Son Samun Nasara, To Ta Sa Mata A Gaba – Amina Soba

by Abdullahi Muhammad Sheka
33 mins ago
0

Hajiya Amina Adamu Soba, Tsohuwar 'yar takara ce a jam'iyyar...

Allurar Rigakafin Kurona

An Yi Kira Ga ‘Yan Nijeriya Da Su Rungumi Allurar Rigakafin Kurona Da Zarar An Fara

by Abdullahi Muhammad Sheka
38 mins ago
0

An yi kira ga al"umar kasar nan su yi amfani...

Next Post
KAROTA

KAROTA Ta Cafke Inyamurin Da Ya Yi Safarar Tabar Wiwi Katon 60 A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version