Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Matsalar Tsaro: Gwamnati Ta Rufe Makarantun Dake Karamar Hukumar Kajuru

by Muhammad
March 18, 2021
in LABARAI
2 min read
Bude Makarantu

Executive Governor of Kaduna State Nasir El-Rufai speaks during an interview with Reuters in Kaduna, Nigeria November 1, 2016. REUTERS/Afolabi Sotunde - S1BEUKTKGYAA

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Shehu Yahaya,

Biyo bayan matsalar garkuwa da dalibai da ’yan bindiga suka kaddamar a Jihar Kaduna, gwamnatin jihar ta bada umarnin rufe daukacin makarantun da suke karamar hukumar Kajuru har sai an samu saukin matsalar tsaro a yankin.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Ilimi ta jihar ta fitar karkashin ofishin kula da ingancin ilimi na ma’aikatar, ta bayyana cewa, rufe makarantun ya zama wajibi bisa matsalar garkuwa da mutane da ake yi a yankin.

Sanarwa mai dauke da sa hannun Abigel Adze ta ce, “daga ranar 16 ga Maris, 2021, mun bayar da umarnin rufe daukacin makarantun da suke karamar hukumar Kajuru nan take, saboda matsalar masu garkuwa da mutane har sai yadda hali ya yi.”

A zantawarsa da Wakilin LEADERSHIP A YAU ta wayar tarho, Kwamishinan Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kaduna, Dakta Shehu Usman Makarfi, ya bayyana cewa, rufe makarantun a halin yanzu shine mafita ga dalibai bisa ganin yadda matsalar sace mutane take kara ta’azzara a wasu sassa na jihar Kaduna.

Kwamishinan ya ce, “Eh, da gaske ne mun bada umarnin rufe daukacin makarantun da suke karamar hukumar Kajuru, saboda kare rayukan dalibai bisa ganin yadda yankin yake fama da matsalar ‘yan bindiga.”

Dakta Makarfi ya kara da cewa, “ba makarantun gwamnatin kadai ba ne aka rufe, har da masu zaman kansu. Saboda haka muna umartar duk shugabannin makarantun da shugabannin malamai da su tabbatar da da cewa, sun bi dokar har sai lokacin da gwamnati ta bayar da sanarwa budewa.”

Ya ce, Gwamnatin Jihar Kaduna tana bakin kokarinta wajen tabbatar da matsalar tsaro ba ta haifarwa harkar ilimi matsala ba yana mai cewa, yanzu haka suna kokarin ganin an kawo karshen matsalar.

karamar Hukumar Kajuru an dade tana fama da matsalar rikice-rikice masu alaka da addini da kabilanci da kuma matsalar ’yan bindiga, wanda ya zama ruwan dare a yankin.

A ranar Litinin din da ta gabata sai da jami’an tsaron soja suka ceto wasu yara guda biyu da suka fada tarkon ‘yan bindiga a kananan hukumar Kajuru da Chikun.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Kaduna Ta Bayyana Ceto Mutane 10 Daga Hannun ’Yan bindiga

Next Post

An Biyo Daliban Da Kwankwaso Ya Tura Karatu Waje Basussuka – Sheikh Khalil

RelatedPosts

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Isra'ila ta ce ta kai harin bama-bamai...

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Wani babban kwamandan ISWAP, Bukar Gana (wanda...

NDLEA

NDLEA Ta Sanar Da Fara Kai Farmaki Dakunan Hada Muggan Kwayoyi

by Muhammad
13 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Shugaban hukuamar NDLEA Birgediya Janar Buba Marwa...

Next Post
Amurka

An Biyo Daliban Da Kwankwaso Ya Tura Karatu Waje Basussuka – Sheikh Khalil

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version