Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Matsalar Tsaro: Majalisar Dattawa Na Neman A Sake Nazarin Yarjejeniyar ECOWAS 

by
1 year ago
in LABARAI
2 min read
Sanatoci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Majalisar dattawa tana neman Nijeriya ta sake nazarin yarjejeniyar shige da ficen da aka kulla tsakanin kasashen Afrika ta yamma wajen shawo kan kwararowar masu aikata laifuka cikin kasar nan, a ranar Laraba.

Majalisar, a bayyana hakan a wata sanarwar manema labarai, mai dauke da sa hannun mai taimaka wa shugaban majalisar- Ezrel Tabiowo ta fannin aikin jarida a Abuja.

Sanata Lawan ya yi kiran a daidai lokacin da yake gargadi dangane da cusa kabilanci a matsalar garkuwa da jama’a hadi da ayyukan ta’addancin yan bindiga dadi a kasar nan. Wanda majalisar ta yi kiran ne a doguwar tattaunawar da ta gudanar a zauren kan kudurin rashin tsaro a fadin Najeriya.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Da yake gabatar da kudurin, Sanata Robert Ajayi Boroffice, daga jihar Ondo (APC), ya bayyana bakin cikin bisa rahotannin kashe jama’a da garkuwa da su a jihohin Ondo, Edo, Oyo, Imo, Kaduna, Zamfara, Niger, Nasarawa, Kebbi da sauran wasu jihohin kasar nan.

Bugu da kari, majalisar ta bukaci mai ba shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, sabbin shugabanin runduninin sojojin Nijeriya da Sufeto Janar na yan sanda, su gaggauta daukar matakan gano hanyoyin canza fasalin tsarin tsaron kasar nan da yadda ma’aikatan tsaro wadanda zasu taimaka wajen shawo kan matsalar musamman a kauyuka.

Haka zalika kuma, zauren majalisar ya yi kira ga gwamnonin jihohi da su mayar da kaimi wajen farfado da ingatattun ayyukan raya yankunan karkara tare da jawo al’umma kusa dasu wajen magance rikicin kabilanci, su kaddamar da sabon tsarin kiwo na zamani domin magance rikici tsakanin makiyaya da manoma.

Har wala yau kuma, majalisar dattawan ta bukaci jami’an tsaro su yi amfani da jiragen sama maras matuki da jirage masu saukar ungulu wajen kula da dazuzzuka, wanda hakan zai taimaka wajen gano mafakar yan bindiga. Sannan kuma ta yi kira ga gwamnatin tarayya ta dauki matakin gaggawa wajen dakile safarar makamai da tabbatar da dokar hana mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

Ahmad Lawan ya gargadi yan siyasa da su guji siyasantar da matsalar tsaro zuwa ga kabilanci saboda kauce wa kawo rikicin da zai kai ga zubar da jini tsakanin kabilun kasar nan.

A karshe ya yi kiran a samar da karin kudade ga sojoji don su samu damar shawo kan matsalar rashin tsaro da ta mamaye dukkan sassan kasar nan.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan Nijeriya Ku Rika Kai Korafinku Ga Majalisa Musamman A Yanzu – Lawan

Next Post

Ya Kamata Gwamnatin Buhari Ta Tallafa Wa Manoman Timatir – Musa Dan Muhammad

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
5 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
7 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
18 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
24 hours ago
0

...

Next Post
Ya Kamata Gwamnatin Buhari Ta Tallafa Wa Manoman Timatir – Musa Dan Muhammad

Ya Kamata Gwamnatin Buhari Ta Tallafa Wa Manoman Timatir - Musa Dan Muhammad

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: