Maigari Abdulrahman">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Matsalar Tsaro: Mutum 25,794 Suka Mutu A Shekara Hudun Mulkin Buhari – Rahoton NST

by Maigari Abdulrahman
June 19, 2019
in LABARAI
2 min read
Shugaba Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Olowo Na Owo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Akalla mutum 25,794 ne su ka rasa rayukansu a cikin shekaru hudu na mulkin shugaban kasa Buhari.

Kididdigar dai na dauke ne a cikin wata sanarwar bayani da wata kungiyar tantance harkar tsaro a  Najeriya wato ‘Nigerian Security Tracker’, wacce ke karkashin kulawar majalisar kula da ayukkan kasa da kasa a kasar Amurka.

samndaads

Adadin dai, na wadanda su ka mutu ne sanadiyar rikicin Boko Haram, kungiyoyon ta’addanci da kuma, wadanda su ka rasa ransu a sakamakon kisan wuce gona da iri na jami’an sojojin Nijeriya.

Daga watan Yunin 2015 zuwa Mayun 2019  a lokacin da Buhari ya karbi mulki kenan, an rasa rayuka a jihar Borno 9,303 kamar yanda wakilinmu ya nazarta, inda jihar Zamfara ke binta da 1,963 sannan jihar Adamawa da 1,529.

A cikin adadin a shekaru hudun, kungiyar Boko Haram ce tai sanadiyar 5,598, inda rikicin fulani makiyaya da sauran fadace-fadace yai sanadiyar 4,917.

A zamanin mulkin Jonathan daga shekarar 2011 zuwa 2015, an kiyasta akalla mutane 34,884 ne su ka mutu a fadin kasar, inda akalla mutum 12,765 su ka mutu imma dai sanadiyar Boko Haram ko kuma sojojin Najeriya.

A yayin da take bayyana madogarar kidayar ta ta, majalisar ta bayyana cewa, ta yi anfani ne da rahotannin kafafen sadarwa a matsayin madogarar tattara kidayar.

“Mun yi anfani da rahotannin kididdigar mako-mako na kafafen sadarwar Najeriya da na kasashen waje,” a cikin rahoton na majalisar.

Ta ci gaba da cewa, “kididdigar ta fara ne daga 29 ga watan Mayun 2011, ranar da aka rantsar da shugaban kasa. Muna daukar kididdigar ne mako-mako.

“Dogaro da rahotannin kafafen sadarwa wurin kididdage wa yana da nashi matsaloli, akwai banbancin samun tabbaci da hakikanin bayanai a tsakanin yankuna, a kan samu rashin takaimaimen adadin wadanda su ka mutu, sannan bayanin yanda abun ya faru ma ya kan babanta.”

Daga karshe, majalisar ta karkare da cewa, “Akwai kuma yiyuwar murda hakikar adadi ko dan saboda dalili na siyasa, kan haka, NST kan nemi bayanai daga majiyoyi daban-daban. Duk da haka dai, rahoto manuniya ce, ba wai hakikar adadin ba.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Wani Wuri Da Bom Ya Tashi A Maiduguri

Next Post

Lauyoyin PDP, APC Sun Jinjina Wa Kotun Sauraron Kararrakin Zaben Gwamnan Bauchi

RelatedPosts

Sarkin Musulmi

Fulani Ba ‘Yan Ta’adda Ba Ne –Sarkin Musulmi

by Maigari Abdulrahman
16 hours ago
0

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya ce...

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

by Maigari Abdulrahman
21 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na...

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

by Maigari Abdulrahman
21 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Mohammed, Matawallen...

Next Post
An Kama Wadanda Suka Kashe Wata Mata A Dakin Otal A JIhar Ebonyi

Lauyoyin PDP, APC Sun Jinjina Wa Kotun Sauraron Kararrakin Zaben Gwamnan Bauchi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version