Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Matsayin Neymar Da Mbappe A PSG

by Abba Ibrahim Wada
December 31, 2020
in WASANNI
2 min read
Neymar Da Mbappe
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tuni wasu rahotanni daga kasar Ingila suka fara bayyana cewa korar da kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German ta yiwa kociyan kungiyar Thomas Tuchel zata iya hana dan wasa Kylian Mbappe komawa Real Madrid a karshen kakar wasa.

A ranar Alhamis din data gabata ne kungiyar kwallon kafa ta PSG ta kori Thomas Tuchel, dan asalin kasar Jamus sanarwar da akasarin kafafen yada labaran Faransa dana nahiyar turai suka yi ta yadawa ta tabbata.

samndaads

Thomas Tuchel na daga cikin mutanen da suka taimakawa kungiyar ta PSG tsawon lokacin da ya share da babbar kungiyar PSG kuma ya lashe kofuna da dama a kungiyar tun bayan komawarsa daga kungiyar Borussia Dortmund ta kasar Jamus.

Rashin lashe kofin zakarun Turai ya sa magabatan kungiyar ta PSG suka yanke shawarar korar Tuchel bugu da kari a wannan kakar wasan kungiyar bata buga abin arziki a gasar lig one ta kasar Faransa kuma tuni kungiyar ta shiga tattaunawa da wani makusancin Tuchel, dan kasar Argentina Mauricio Pochettino.

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid dai tayi alkawarin sayan dan wasa Mbappe idan an kammala kakar wasan bana wanda hakan ne yasa kungiyar bat sayi dan wasa ko daya ba a kasuwar data gabata saboda tana tara kudin sayan Mbappe.

A kwanakin baya dan wasan shima ya bayyana cewa bashi da burin ci gaba da zaman kungiyar kuma yana fatan a karshen kakar wasa zai koma daya daga cikin kungiyoyi manya a nahiyar turai.

Shi ma dan wasa Neymar, wanda baiji dadin korar da akayiwa Tuchel ba, yana bukatar tsayawa domin karatun ta nutsu akan yanayin da kungiyar zata kasance nan gaba duba da har yanzu ba’a san wanda kungiyar zata dauka ba.

A kwanakin baya Neymar ya bayyana cewa zai iya barin kungiyar ta PSG idan har shugabannin kungiyar ba suyi kokarin sayo dan wasa Messi ba wanda yake shirin barin Barcelona a karshen kakar wasa ta bana.

Sai dai PSG za ta fuskanci kalubale daga wajen wasu daga cikin manyan kungiyoyi kamar Manchester City, wadda kociyan kungiyar yake da alaka mai kyau da Messi sai kuma kungiyoyin Chelsea da Inter Milan.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Waye Gwani Tsakanin Anthony Joshua Da Tyson Fury?

Next Post

Yadda Atletico Madrid Ta Sahale Kwantiraginta Da Diego Costa

RelatedPosts

Lampard

Ana Dab Da Korar Lampard A Chelsea

by Abba Ibrahim Wada
12 hours ago
0

Rahotanni daga kasar Ingila sun bayyana cewa shugabannin kungiyar ta...

Dele

Cinikin Dele Alli: PSG Ta Fara Magana Da Tottenham

by Abba Ibrahim Wada
12 hours ago
0

Dan wasan tsakiya na kungiyar kwallon kafa ta Tottenham Dele...

Copa

Gasar Copa Del Rey: Real Madrid Ta Yi Abin Kunya

by Abba Ibrahim Wada
12 hours ago
0

Real Madrid  ta buga gasar cin kofin Copa del Rey...

Next Post
Diego Costa

Yadda Atletico Madrid Ta Sahale Kwantiraginta Da Diego Costa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version