Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Matsin

Hukumar Kare Hakkin Bil’adama (NHRC), ta ce matsin rayuwa ta sa magidanta 106 a Jihar Gombe sun yi watsi da kula da ‘ya’yansu a shekarar da ta wuce.

Jami’in watsa labarai na hukumar, Ali Alola-Alfinti, shi ne ya shaida hakan ga kamfanin dillacin labarai ta kasa a Gombe.

Ya Kamata Sin Da Faransa Su Ba Da Jagora Wajen Yin Mu’amala A Shekaru 60 Masu Zuwa

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Ya nuna damuwa kan karuwar yasar da yara da ake samun yi a Jihar Gombe, inda ya ce, hukumar ta damu matuka da hakan.

Mista Alola-Alfinti, ya ce, cikin korafe-korafe 280 da suka amsa a 2023, guda 106 na watsar da yara ne, da ke nuni da kaso 37.9 cikin dari na korafe-korafen da suka sauma a cikin shekarar.

Ya ce, watsar da yara na samuwa ne sakamakon yadda iyaye ke kaurace wa nauyin da ke kawukansu.

Ya kara da cewa a lokacin da uba ya kasa samar da kulawar da ta dace wa ‘ya’yansa, hakan zai kai ga zaman yaron wanda aka yi watsi da shi da fita sha’aninsa, kuma hakan zai iya shafan kiwon lafiyarsa da ma ta kwakwawarsa.

Ya ce, “Magidancin da ya yi watsar da ‘ya’yansa da matansa ba tare da abinci ba, babu kulawa babu sauran abubuwan bukata na rayuwa, mun samu kesa-kesai guda 106 na yaran da aka yi watsi da lamarinsu a 2023, sakamakon matsin rayuwa, wanda shi ne kaso mafi tsoka da muka amsa.

“Babban dalilin da ke janyo faruwar wannan lamarin shi ne matsin tattalin arziki, iyaye da dama ana daura musu laifin ne sakamakon halayensu na ko-in-kula.”

Ya ce, yaran da aka watsar nauyi ne a kan al’umma su kula da su domin guje wa gurbacewar rayuwarsu balle su zo su zama abun damuwa ga al’umma. Inda ya yi bayanin cewa masu ruwa da tsaki ya dace su shawo kan wannan matsalar.

A cewarsa, hukumar NHRC za ta kara azama wajen wayar da kan jama’a tun daga matakin farko kan wannan lamarin domin ganin iyaye suna daukan nauyin da ke kawukansu da muhimmanci na kula da rayuwar ‘ya’yansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani

Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version