Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Matsin Tattalin Arziki Ne Ya Tilasta Min Saida Jaririna, Cewar Wata Uwa

by
1 year ago
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Jaririna
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Khalid Idris Doya

Wata uwa ‘yar shekara 21 a duniya, Emila Sunday, an cafketa bisa zargin yunkurin saida jaririnta dan watanni uku a duniya a Ojoto da ke karamar hukumar Idemili ta Kudu da ke jihar.

Wacce ake zargin ‘yar asalin jihar Akwa Ibom ce, an bada rahoton cewa ta yi yunkurin saida karamin yaronta a kan kudi naira N150,000.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Ta nuna cewa ta aikata hakan ne bisa tsananin talauci da fatara da ta fada.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin ‘yan sandan jihar Haruna Muhammad, ya shaida cewar an kame wanda ake zargin ne da yammacin ranar Talata a yanki.

Ya ce: “A ranar Talata da karfe shida na yammaci, biyo bayan samun rahotonnin sirri, jami’an ‘yan sanda da ke aiki a karkashin caji ofis din Ojoto da ke Anambra, sun cafke wata mata mai suna Emila Sunday wacce ta yi ikirarin cewa ita ‘yar jihar Akwa Ibom ce mai shekarun haihuwa 21 a duniya, da danta ‘yar wata uku a kauyen Ire Ojoto.

“Binciken farko-farko ya nuna cewa matar ta yi kokarin saida danta, dan wata uku da ta yi ikirarin cewa matsatsin rayuwa ne ya sanyata hakan.”

Haruna Muhammad ya shaida cewar an samu nasarar ceto yaron cikin kwashin lafiya, yana mai karawa da cewa bincikensu na cigaba da gudana domin gano yadda lamarin ya ke.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Hada Kai Da Cigaban Sana’armu Ne Manufar Kungiyarmu – Shugaban Kungiyar ’Yan Tifa

Next Post

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Kara Damara Wajen Gyara Tarbiyar Matasa – Imam Suleman Ibrahim

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Imam Suleman

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Kara Damara Wajen Gyara Tarbiyar Matasa - Imam Suleman Ibrahim

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: