Mayar Da CBN Legas: Muna Roko A Mayar Da Ma'aikatar Kasuwanci Kano, NNPCL, NIMASA, NPA Zuwa Neja Delta
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mayar Da CBN Legas: Muna Roko A Mayar Da Ma’aikatar Kasuwanci Kano, NNPCL, NIMASA, NPA Zuwa Neja Delta

bySulaiman
2 years ago
CBN

Tsohon Mataimakin Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Kasa, Hon. Yekini Nabena, ya bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya amince da mayar da kamfanin man fetur na kasa (NNPCL) zuwa yankin Neja Delta.

Ya kuma bukaci Tinubu da ya mayar da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya zuwa jihar Binuwai inda amfanin noma ke da yawa don yin daidaito kan kudirin mayar da wasu sassan babban bankin Nijeriya (CBN) da hukumar kula da filayen tashi da saukar jiragen sama ta kasa FAAN daga Babban Birnin Tarayya (FCT) zuwa Legas.

  • Tinubu Ya Tafi Faransa Domin Yin Wata Ziyarar Sirri
  • Ba Mu Kama Shugaban Miyetti Allah Ba – DSS

Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu, ta nuna sha’awarta na maida wani bangare na CBN da FAAN zuwa jihar Legas, ta ce, hakan zai fi da cewa. Duk da cewa, yunkurin ya jawo mahawara mai zaifi na daga goyon baya da adawa, musamman daga bangaren Arewacin Nijeriya.

Nabena, wanda ke zargin munanan manufar yin irin wannan yunkuri, ya ce, Shugaba Bola Tinubu tuni dama bai yi imani da kasancewar Nijeriya a matsayin kasa daya ba kafin ya zama shugaban kasa.

Jigon na APC a wata sanarwa da ya fitar a Abuja ranar Laraba, ya nanata cewa, hukumomin tarayya alamomin hadin kan Nijeriya ne kuma bai kamata a yi wasa da su ba.

Nabena ya ce: “Idan har ingancin wadannan sassa a ka duba don mayar da su inda ya fi da cewa (Legas), mu ‘yan yankin Neja Delta muna rokon cewa, NNPCPL, NIMASA, NPA da sauran su za su fi da cewa a jihohin Bayelsa, Rivers ko Delta.

“Haka zalika ma’aikatar ma’adinai da karafa ta tarayya ta koma jihar Kogi inda muke da Babbar masana’anta ta Karfe da ke Ajaokuta.

“Na kuma yi imanin cewa, ko dai a mayar da ma’aikatar ciniki da zuba jari ta tarayya zuwa Kano ko kuma a mayar da ita jihar Anambra inda ake da manyan kasuwanni, haka ma a kai ma’aikatar noma ta tarayya jihar Binuwai, domin takenta shi ne ‘kwandon abinci na Kasa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
Sudan: Aiwatar Da “Yarjejeniyar Jiddah” Za Ta Shimfida Zaman Lafiya – Gwamnati

Sudan: Aiwatar Da “Yarjejeniyar Jiddah” Za Ta Shimfida Zaman Lafiya - Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version