Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?

byCGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
FOCAC

Tun daga farkon wannan mako, Beijing, babban birnin kasar Sin ya fara karbar baki daga kasashen Afrika da suka hada da shugabannin kasashe da gwamnatoci da ma manyan jami’ai, da suka zo domin halartar taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen nahiyar Afrika wato FOCAC. A bana, Beijing zai sake ganin haduwar shugabannin bangarorin biyu, bayan wanda aka yi a shekarar 2018. 

 

Dandalin FOCAC dai ya zama wata laima da hadin gwiwar Sin da Afrika ke fadada karkashinsa, duba da irin alfanun da yake tattare da shi. Tun bayan kafuwarsa shekaru 25 da suka gabata, har kullum dandalin na nacewa ne ga ka’idojin gudanar da tsare-tsare tare, samun ci gaba tare da ma moriyar juna tsakanin bangarorin biyu.

  • An Gudanar Da Taron Ministoci Na Dandalin FOCAC Karo Na 9 A Beijing
  • NNPC Ya Ƙara Farashin Man Fetur Zuwa 855 Kan Kowace Lita 

Me ya sa dandalin da ma dangantakar Sin da Afrika ke samun karbuwa?

 

A duk lokacin da aka ambaci kasar Sin, ba shakka abun da zai zo ran al’ummar Afrika shi ne, taimakon kasar gare su. Tabbas kasar Sin ta zama aminiya ta kwarai mai taimako ba tare da la’akari da ana cikin wuya ko dadi ba, kana ba tare da wani sharadi ko yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashen Afrika ba. Taimakon kasar Sin ya isa lungu da sako da kowanne bangare na Afrika. Kama daga ababen more rayuwa zuwa kiwon lafiya da tallafin ilimi da cinikayya da horo da abinci da sauransu.

 

Na yi imani a cikin lokacin da aka dauka ana hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu, ta samar da taimako na zahiri da manyan kasashe masu mulkin mallaka ba su samar ba, tsawon lokacin da suka dauka suna mamaya a nahiyar Afrika.

 

Hausawa kan ce, ruwan da ya dauke ka, shi ne ruwa. Ina da yakinin babu wani mutum daga nahiyar Afrika da bai ci moriyar wani abu daga kasar Sin ba. Jama’ar Afrika, sun gani kuma sun shaida huldar Sin da kasashensu, sun kuma ga alfanunta a zahiri, shi ya sa kasar Sin ke kara samun karbuwa a wajensu. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Kasashen Yamma Na Yunkurin Cimma Burinsu Ta Hanyar Goyon Bayan Philiphines

Kasashen Yamma Na Yunkurin Cimma Burinsu Ta Hanyar Goyon Bayan Philiphines

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version