Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Bayyana Cikakken Dalilin Kafa Askarawan Kare Ma’adanai

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Ma'adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake ya karbi bakuncin rukuni na farko na Askarawan kare ma’adanai da aka kafa kwanan nan domin su yi aikin kare wuraren da ake hakar ma’adanai a sassan kasar nan.

An kafa Askarawan ne a karkashin jagorancin shugaban hukumar tsaron farin kaya (NSCDC), Abubakar Audi. A ranar 1 ga watan Maris ne Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ya kaddamar da rundunar don su yi aikin kawo karshen masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a sassan Nijeriya, wanda hakan ake sa ran zai inganta kudaden shiga a bangaren tattalin arzikin Nijeriya.

  • Ba Ka Da Aiki Sai Yin Barci A Abuja – Martanin Ɗan El-Rufai Ga Uba Sani
  • El-Rufai Ya Jibge Min Bashin $587 Da Biliyan 85 A Kaduna – Uba Sani

Kaddamar da dakarun ya yi daidai da bikin ranar da majalisar dinkin duniya ta ware don bikin ranar kula da hakkin fararen hula a duniya, wanda aka yi a Abuja.
Ma’aikatar ma’adanai ne ta su kula da ayyukan Askarawan.

An shirya cewa, za a tattaro dakarun ne daga jihohin tarayyar Nijeriya da babban birnin tarayya Abuja inda a halin yanzu aka kafa runduna mai mutum 60.

Alake ya umarci dakarun su tabbatar da sun kawo karshen sace-sace da ayyukan ta’addanci da ke faruwa a wuraren hakar ma’adanai a sassan Nijeriya.

Minista Alake ya kuma yaba wa Minista Olubunmi-Ojo a kan yadda ya tsayu na ganin an samu nasarar kafa rundunar.

“An kaddamar da Askarawan ne tare da hadin gwiwar ministan cikin gida don kare wuraren hakar ma’adanai, ta haka za a tabbatar da cin gajiyar albarkatun ma’adanai da Allah ya shinfida a sassan Nijeriya.Wannan kuma na daga cikin shirye-shiryen da Shugaba Tinubu ya yi na bunkasa bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya, ”Kamar yadda Segun Tomori mai ba Minista Alake shawara a kan harkokin yada labarai ya bayyana a sanarwa da ya raba wa manema labarai.

“Ina mai farin cikin sanar da al’umma cewa, an kafa dakarun ne don tsaftace wuraren hakar ma’adanai daga matsalar tsaro, mun kuma samu nasarar kafa rukuni na farko na jami’an da za su yi wannan aikin kamar yadda muka kaddamar a yau.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

Bassirou Diomaye Faye: Daga Kurkuku Ya Zama Shugaba Mafi Karancin Shekaru A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version