Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Nemi A Ƙara Ƙulla Danƙon Zumunci A Tsakanin Nijeriya Da Kamfanin BBC

bySulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira da a zurfafa alaƙa tsakanin Nijeriya da BBC domin samar da al’umma mai masaniya a kan harkokin yau da kullum.

 

Idris ya bayyana haka ne a wata ziyara da ya kai hedikwatar BBC da ke birnin Landan.

  • An Bude Baje Kolin Manyan Bayanai Na Kasa Da Kasa A Kasar Sin
  • NCC Ta Tsawaita Haɗa Lambar NIN Da Layukan Waya Zuwa Watan Satumba

Ziyarar dai wani ɓangare ne na ƙoƙarin samar da kyakkyawar alaƙa tsakanin Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Nijeriya da kafafen yaɗa labarai daban-daban, na gida da waje.

 

A ziyarar,  an yi nasarar ganawa da manyan shugabannin BBC, ciki har da Mataimakin Shugaban Sashen Yaɗa Labarai na BBC kuma Daraktan BBC, Jonathan Munro.

 

Idris ya jaddada muhimmancin kafafen yaɗa labarai wajen tsara fahimtar jama’a da haɓaka ci gaba.

 

Ya ce: “Kafofin watsa labarai suna taka rawa mai muhimmanci wajen tsara labaran da suka dace, da samar da fahimtar juna, da samar da cigaba, don haka ya zama wajibi ga kafafen yaɗa labarai da ke isar da saƙo ga duniya su zurfafa fahimtar yanayin zamantakewa da siyasa da tattalin arziki da al’adun al’ummomin da suke ba da rahoto akai.”

 

Idris ya kuma bayyana muhimmancin rawar da BBC ke takawa wajen bayar da rahotanni kan tafiyar siyasar Nijeriya, yana mai cewa yana da muhimmanci BBC ta daidaita rahotannin da take yi kan Nijeriya ta hanyar mai da hankali kan cigaban da ƙasar ke samu.

 

Ya ƙara da cewa, “Nijeriya tana da ɗimbin matasa masu tasowa da ƙaunar da ba a saba gani ba na cin gajiyar damarmaki ko da kuwa ana fuskantar ƙalubale masu tarin yawa, lamarin da ke buƙatar a ba da muhimmanci ga sakamako mai kyau a Nijeriya.”

 

Ya kuma yi nuni da cewa yaɗa labaran ƙarya babbar matsala ce da ke kawo cikas ga cigaba da kuma lalata amanar da ke tsakanin gwamnati da jama’a.

 

Idris ya yi kira ga BBC da ta yi aiki tare da abokan hulɗar ta na ƙasa da ƙasa don magance waɗannan matsalolin.

 

Ministan ya yaɓa da yadda BBC ke faɗaɗa ayyukan su a Nijeriya ta hanyar samar da ƙarin yarurrukan da suke gabatar da shirye-shirye da su, wato Hausa, Ibo, Yarbanci, da Pijin.

 

Ya ce hakan ya taimaka wajen yaɗa bayanai da yawa tare da samar da ayyukan yi ga ‘yan Nijeriya da dama.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Za Mu Tabbatar An Yi Zaben Gwamnoni Lafiya Ba Tare Da Tangarda Ba A Kebbi – ‘Yansanda

‘Yansanda Sun Yi Allah-Wadai Da Kisan Gillar Da Sojoji Suka Yi Wa DPO Wasagu A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version