Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Kare Haƙƙoƙin Naƙasassu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Kare Haƙƙoƙin Naƙasassu

bySulaiman
1 year ago
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ba da umarnin kafa wani kwamiti mai mutum biyar da zai fito da tsarin aiki da Hukumar Naƙasassu ta Ƙasa domin wayar da kan jama’a game da ‘yanci da kuma damarmakin naƙasassu.

Ministan ya bayar da umarnin ne a Abuja a ranar Laraba a lokacin da ya karɓi baƙuncin Babban Sakataren Hukumar Nakasassu, Dakta James Lalu, a wata ziyarar ban-girma da ya kai ofishin sa.

  • Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 
  • Ministan Harkokin Wajen Gabon Ya Yabawa Nasarorin Da Gabon Da Sin Suka Samu A Fannonin Sada Zumunta Da Hadin Gwiwa

Ya ce: “Daga yau, za mu kafa kwamitin da zai yi aiki kafaɗa da kafaɗa da ku don duba takamaiman buƙatun ku domin mu taimaka wajen ganin an cimma manufofin ku.”

Idris ya ƙara da cewa zai ba hukumar damar yin aiki da hukumomin yaɗa labarai da kayan aikin ma’aikatar sa domin kare haƙƙi da mutuncin naƙasassu da kare su daga wariya.

Ministan ya ce Shugaba Tinubu ya yi imani da haɗin kan jama’a, don haka ya jajirce wajen ba da ganuwa, karɓuwa, da alhaki ga naƙasassu a gwamnatin sa.

Ya ƙara da cewa, “Babu wani ɓangare na al’ummar Nijeriya da za a bari a baya a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu.”

Ya yi alƙawarin jagorantar kai shawarwari ga gwamnonin jihohi game da tsarin doka na naƙasa a jihohin su.

A nasa jawabin, Dakta Lalu ya ce ya je ma’aikatar ne domin neman haɗin gwiwa domin wayar da kan jama’a kan haƙƙin naƙasassun.

Ya ce wasu sassan Dokar Naƙasa sun umurci masu ba da sabis da su samar da dama ta musamman ga naƙasassu a wurare kamar gine-ginen jama’a, sufuri, da wuraren kula da lafiya da sauran su ba tare da nuna wariya ba.

Dakta Lalu ya ce naƙasassu na da ɗimbin damarmaki waɗanda suka haɗa da fasahohi daban-daban, cancanta, da basirar da ake buƙata don cigaban tattalin arzikin ƙasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
matsinn rayuwa

Duk Da Matsin Rayuwa: Hukumomi 7 Sun Kebe Wa Kansu Naira Biliyan 80.9 Na Jin Dadi

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version