CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

MOC: Yawan Albarkatun Noma Da Sin Ke Shigowa Da Su Daga Afirka Na Kara Fadada

by CRI Hausa
January 15, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
MOC: Yawan Albarkatun Noma Da Sin Ke Shigowa Da Su Daga Afirka Na Kara Fadada
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin, ta ce yawan albarkatun gona da Sin ke shigowa da su daga kasashen Afirka na kara fadada, inda a watannin 11 na farkon shekarar 2020 da ta gabata, adadin ya karu da kaso 4.4 bisa dari, wanda kuma hakan ya nuna dorewar wannan ci gaba cikin shekaru 4 a jere.

samndaads

Da yake karin haske game da hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a jiya Alhamis, kakakin ma’aikatar cinikayyar Gao Feng, ya ce cikin watannin 11, jimillar kudaden cinikayyar sassan biyu ta kai dalar Amurka biliyan 167.8.
Gao ya ce kasar Sin ce babbar abokiyar huldar cinikayyar nahiyar Afirka cikin shekaru 11 a jere, inda ta zamo ta biyu wajen shigo da albarkatun gona daga nahiyar.
Kaza lika jami’in ya ce, Sin ta tallafawa nahiyar a fannin gina layukan dogo da manyan titunan mota da suka kai tsawon sama da kilomita 6,000, da kuma kusan tashoshin ruwa 20, da sama da manyan ayyukan samar da lantarki 80. Sauran sun hada da sama da cibiyoyin kiwon lafiya 130, da filayen wasa 45 da kuma makarantu 170.
A daya hannun kuma, kamfanonin Sin sun samar da guraben ayyukan yi sama da miliyan 4.5 a kasashen nahiyar. Kaza lika Sin za ta ci gaba da karfafa tushen hadin gwiwar ta da kasashen Afirka, da marawa ci gaban nahiyar baya, tare da gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga kowa karkashin hadin gwiwa da kasashen nahiyar ta Afirka. (Mai fassara: Saminu)

SendShareTweetShare
Previous Post

Kara Gudanar Da Ayyuka Masu Amfani Don Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Next Post

Babban Sabani A Tsakanin Jam’iyyun Amurka Zai Lalata Harkokin Kasa

RelatedPosts

A Shirye Sin Take Ta Karfafa Musayar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Amurka

A Shirye Sin Take Ta Karfafa Musayar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Amurka

by CRI Hausa
4 hours ago
0

Daga CRI Hausa Ministan cinikayya na kasar Sin, Wang Wentao...

Bukatar Ma je Hajji Sallah

Bukatar Ma je Hajji Sallah

by CRI Hausa
4 hours ago
0

Daga CRI Hausa Da alamun har yanzu wasu kasashen yamma,...

Sin Tana Adawa Da Yadda Birtaniya Ta Yi Amfani Da Dandalin UNHRC Domin Shafa Mata Bakin Fenti

Sin Tana Adawa Da Yadda Birtaniya Ta Yi Amfani Da Dandalin UNHRC Domin Shafa Mata Bakin Fenti

by CRI Hausa
5 hours ago
0

Daga CRI Hausa Yau Laraba yayin taron ganawa da manema...

Next Post
Babban Sabani A Tsakanin Jam’iyyun Amurka Zai Lalata Harkokin Kasa

Babban Sabani A Tsakanin Jam’iyyun Amurka Zai Lalata Harkokin Kasa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version