Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Mu Hada Kai Don Ci Gaban Jihar Kano – Sarki Muhammadu Sunusi

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
Idan Ba A Dau Mataki Ba… Za A Fuskanci Annobar Da Ta Fi Boko Haram -Sarki Sanusi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi na biyu, ya jagoranci yiwa gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje addu’a ta musamman a babban Masallacin Juma’ar Kano bayan da ya lashe zaben gwamnan jihar kano a karo na biyu.

Daga cikin wadanda suka halarci taron addu’ar  sun hada da Dagatai, manyan Limamai, Malamai, manyan ma’aikatan gwamnatin jihar, masu bada shawara ta musamman da sauran al’umma.

A cewar sarkin, addu’ar ta neman kariya ce da neman jagorancin Allah a mulkin da gwamnan zai yi karo na biyu da ma kasa baki daya.

Labarai Masu Nasaba

Mai Yuwa A Gaza Kawo Karshen Yaki Da Yunwa A Nijeriya Har Zuwa 2025 —Mata Manoma

Sojoji Sun Kashe 2 Tare Da Tarwatsa Sansanin Bayar Da Horo Na IPOB A Jihar Imo

Mai martaba ya bayyana cewa; yafiya wajibi ce a dukkan wani abu da ya shafi shugabannci da mu’amala da mutane.

ADVERTISEMENT

‘Ba laifi bane wani ya rike ra’ayin shi akan abun da yake faruwa a cikin al’umma, amma abun da ya zama dole bayan zabe shine mutane su hada kansu wajen tabbatar da mulkin wanda yayi nasara.

‘Saboda haka, ya zama wajibi gwamnatin Ganduje ta samu goyan baya da hadin kan al’umma dan cigaban jihar mu.

‘Dole sai mun hada kan mu da cigaban jihar Kano. Sai mun yi aiki tukuru da kuma dagewa da addu’a dan cigaban jihar mu da kasa baki daya.’ inji shi

Ya yi kira ga gwamnan da ya dinga yin bincike a dukkan wani labari da yaji dan wani lokacin mutane suna kirkirar labarai sannan su fara yada jita jita dan sun haifar da rikici.

Mai Martaba ya kara da cewa; Wani lokacin mutane sukan yi abu ba tare da sanin ka ba amma sai wasu su fara yada jita jitan cewa kai ka shirya wannan abun, kuma alhalin baka da masaniya akan abun, sabodahaka, mu ci gaba da yiwa Kano adduár zaman lafiya, ya kuma kara da cewa shugaba dole ya zama na kowa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Samar Da Cibiyar Sarrafa Kashu A Jihohi Hudu  –Ministan Noma

Next Post

Gbajabiamila Ya Shiga Sahun Masu Neman Matsayin Kakakin Majalisar Wakilai 

Labarai Masu Nasaba

Mai Yuwa A Gaza Kawo Karshen Yaki Da Yunwa A Nijeriya Har Zuwa 2025 —Mata Manoma

Mai Yuwa A Gaza Kawo Karshen Yaki Da Yunwa A Nijeriya Har Zuwa 2025 —Mata Manoma

by Abubakar Abba
8 hours ago
0

...

Sojoji Sun Kashe 2 Tare Da Tarwatsa Sansanin Bayar Da Horo Na IPOB A Jihar Imo

Sojoji Sun Kashe 2 Tare Da Tarwatsa Sansanin Bayar Da Horo Na IPOB A Jihar Imo

by Abubakar Abba
8 hours ago
0

...

CAN Ta Shirya Zanga-Zangar Yin Allah Wadai Da Kisan Deborah A Duk Jihohin Nijeriya

Batanci: CAN Ta Janye Gabatar Da Zanga-Zangar Da Ta Shirya Kan Kisan Deborah

by Leadership Hausa
12 hours ago
0

...

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

‘Yan Bindiga Sun Fille Kan Wani Dan Majalisa A Jihar Anambra

by Abubakar Abba
13 hours ago
0

...

Next Post
Gbajabiamila Ya Shiga Sahun Masu Neman Matsayin Kakakin Majalisar Wakilai 

Gbajabiamila Ya Shiga Sahun Masu Neman Matsayin Kakakin Majalisar Wakilai 

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: