Sister Iyami Jalo Turaki">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home CIWON 'YA MACE

‘Mu Ji Tausayin Raunana Sai Allah Ya Ji Tausayinmu’

by Sister Iyami Jalo Turaki
April 24, 2020
in CIWON 'YA MACE
3 min read
‘Mu Ji Tausayin Raunana Sai Allah Ya Ji Tausayinmu’
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Assalamu Alaikum warahmatullah. Godiya ta tabbata ga Allah mai kowa da komai.

Zan yi amfani da wannan dama, musamman bisa la’akari da irin yanayi na annoba da muka tsinci kanmu ciki ahalin yanzu .
Wannan annoba ta cutar Korona,  annoba ce da ta zagaye duniya gabaki dayanta.
Tabbas idan muka yi la’akari  da illar da ta yi ga kasashen da suka ci gaba toh ya kamata mu kiyaye da bin shawarwari da bin dokokin masana da gwamnati domin mu kauce wa fadawa irin halin da wadancan kasashe suka fada. .
Mun yi matukar yabawa da kokarin gwamnati  na kokarin kare rayuwaka da lafiyar al’ummah.
Bin wannan doka ita ce mafita da yardar Allah, toh amman idan muka duba za mu ga mafi yawancin mutanen dake kasar nan musamman  yankin Arewacin Nijeriya   suna rayuwa ne a kan sai sun fita sannan su samo abin da za su ci da iyalansu.
Mu yiwa kawunanmu tambaya akan to su wayyannan mutane me za su ci ko yaya za su yi idan har basu fita neman ba?
Tabbas gwamnati  da masu hannu da shuni da kungiyoyin sa-kai suna kokari, amma mu sani wannan ba hakkin gwamnati  bane ko masu kudi akwai hakki ne daya rataya akan kowa muddin kana da iko komi kankantarshi, toh ina ganin ya wajabta mu fito mu taimaki masu raunin cikinmu.
Idan Kana da niyyar taimako, toh kana yin sa ne daidai ikon ka.
Misali da ni kaina a nan, malamar makaranta ce toh amman sai na ga idan har zan iya ajiye ragowar kudi sai nike ganin tabbas na yi rashin imani kuma na so kaina da yawa idan har akwai wani a kusa da ni da ke jin yunwa a irin yanayin da muka tsinci kanmu, in da na yi amfani da albashina na watan maris wajen siyan kayan tallafi ga ‘yan’uwa da makwabta na kusa da nesa.
Sai na fahimci a cikin masu tururuwar zuwa neman sadakar akwai wadanda suka fi ni da yawa. Tabbas na dada fahimtar cewa akwai mabukata dayawa, Sannan kuma mai hali baya hakuri yabarwa Mara hali .
Wannan dalili yasa mukayi shawarar kafa kwamiti me suna “taimakon mabukata” watau a turance muka kirashi (help the needy) a karkashin kungiyar sulhu da kyautata zamantakewar iyali (help for bictims of matrimonial Abuse foundation)
Mun kudurci anniya da yardar Allah daukar nauyin ciyar da gidajen da suke matukar bukata ta la’akari da yadda za mu shiga watan Ramadan kuma kudurinmu ba zai tsaya a iyakacin Ramadan ba insha Allahu.
Yawan gidajen da za mu dauke wa nauyin ciyarwar zai dangantane da karfin asusunmu tun daga ranar da aka fara azumin watan Ramadan har karshensa da iznin Allah.
Daga karshe ina kira ga mutane da  mu sani cewa ba wai sai muna da kudi za mu iya taimaka wa junnanmu ba, idan kana da abincin gobe to mu duba wanda ba shi da na cin yanzu domin goben Allah ke da ita. Mu sani cewa hannun mikawa ya fi na karba.
Wadanda gwamnati  ke bawa tallafi su raba da su ji tsoron Allah gurin sauke nauyin da aka dora musu su tabbatar da sakon ya kai inda ya kamata ya je.
Idan muna da abincin yanzu  toh mu yi hakuri mu bar wa wanda bai da na yanzu ya karba.
Wata shawara ga maniyyata Umurah da Aikin Hajji ita ce,  tun da a bana saboda lalura da wuya wadannan ibadun su yiwu, toh ga wani aikin Allah idan har domin neman yardar Allah muke yi toh mu fito da kudaden nan domin rage wa mutane kunci da radadin rashin da suke ciki.
Mu sani cewa dukkan wanda ya fidda wani mumini daga kunci toh tabbas Allah zai yaye nasa ya sa masa albarka.
Daga karshe ina kira ga al’ummah da wallahi mu koma ga Allah mu kyautata zukatanmu, mu dimanci istigfari, mu kiyaye zalunci, ko hakan ya taimaka wajen kawar da fushin Allah a kanmu.
Muna addu’a Allah ya bamu ikon sauke nauyin da muka dauka, da fatan Allah ya biya dukkanin wadanda suke da hannu wajen taimakawa al’ummah ta kowace fuska, Allah ya biya su ya ninka masu da mafiyin alkhairi a duniya da lahira, amin summa amin.
Zainab Mohammed
Shugabar Gidauniyar Taimakon Mabukata ta ‘Help the Needy’.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Mata Za Su Mori Wannan Lokaci Da Mazajensu

Next Post

Maraba Da Ramadan: Shawarwari Na Musamman Ga Mata 

RelatedPosts

Kwai

Lafiya Jari: Alakar Cin Kwai Da Ciwon Zuciya

by Sister Iyami Jalo Turaki
16 hours ago
0

Daga Zanna Mustapha Wakili da Muhammad Zahraddin,  Kwan kaji na...

Maganin Zubar Da Ciki

Illar Shan Maganin Zubar Da Ciki (Self Induction)

by Sister Iyami Jalo Turaki
1 week ago
0

Zubar da ciki, ko tada nakuda da kanki ko kuma...

Zubar Da Ciki

Matsalolin Da Ke Biyo Bayan Zubar Da Ciki Ko Barin Ciki

by Sister Iyami Jalo Turaki
3 weeks ago
0

Zubewar ciki ko wanda aka yi da gangan ko wanda...

Next Post
Maraba Da Ramadan: Shawarwari Na Musamman Ga Mata 

Maraba Da Ramadan: Shawarwari Na Musamman Ga Mata 

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version