Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

bySulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cew a za ta ci gaba da bin umarnin da kowace kotu ta bayar a dukkan hukunce-hukuncen da su ka shafi zaɓe.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke jawabi wurin buɗe Taron Alƙalai na Ƙara wa Juna Ilmi Kan Zaɓen, wanda aka yi ranar Litinin a Cibiyar Inganta Harkokin Shari’a (NJC), a Abuja.

  • Mutum Miliyan 93.5 Ne Za Su Kada Kuri’a A Zaben 2023 – INEC

Ya ce: “An shirya irin wannan zama kafin zaɓen 2019, inda aka yi bitar rikice-rikicen ƙararrakin da za su taso bayan zaɓe. Kuma wancan taron da mu ka yi ya yi tasiri sosai a lokacin.

“Saboda an samu raguwar hukunce-hukuncen da kotuna ke bayarwa masu cin karo da juna. Kuma an samu raguwar yawan zaɓen da kotuna ke sokewa masu yawan gaske.”

Yakubu ya gode wa manyan alƙalai da Hukumar Kula da Shari’a ta Ƙasa dangane wannan taro mai muhimmanci, wanda ya ce babu shakka zai rage yawan ƙararrakin zaɓe a kotuna.

INEC

Dangane da muhimmancin taron, Yakubu ya buga misali da irin matsalolin da ake samu a kotuna dalilin yanke hukunci masu karo da juna da kotuna ke yi.

Ya ce, “An samu wata kotu ta yi fatali da hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke, ta umarci INEC ta bayar da satifiket ɗin nasarar zaɓen fidda gwani ga ɗan takarar da Kotun Ƙoli ta soke zaɓen sa. To kun ga wannan cikas ne sosai ga hukumar zaɓe.

“Irin wannan kuma shi ke haifar da cinkoson shari’un zaɓe a kotu. Kuma an maida hannun agogo baya, tunda an sake shari’ar kenan wataƙila ma har sai an kai ga komawa Kotun Ƙoli.”

Haka kuma shugaban na INEC ya nuna damuwa dangane da yawaitar ƙararrakin da aka haɗa da aka da sunan INEC aka maka kotu har sama da 600, a zaɓen fidda gwanin ‘yan takarar jam’iyyu daban-daban.

Yakubu ya bayyana cikin damuwa cewa: “Ko kwanan nan wata jam’iyya ta zo a rana ɗaya ta kawo mana sunayen sabbin ‘yan takara 70 da ta ke so a cire sunayen na farkon da aka aiko mana, a maye gurbin su da sabbin da su ka kai mana.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

ICPC Ta Fara Binciken Ayyukan Mazabun Tarayya A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version