Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home TATTALIN ARZIKI

Mun Raba Naira Tiriliyan 1.5 Ga Manoman Nijeriya, Cewar CBN

by Sulaiman Ibrahim
March 29, 2021
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Rubutun Ajami
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad

 

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya ce ya raba Naira Tiriliyan 1.487 a karkashin shirinsa na habaka noma don bunkasa wadatar abinci.

Gwamnan Babban Bankin, Godwin Emefiele, ya bayyana haka yayin gabatar da sanarwar game da taron Kwamitin manufofin kudi (MPC) wanda aka gudanar a ranakun Litinin da Talata a Abuja.

Emefiele ya ce, bankin koli ya raba naira biliyan 107.60 ga manoma 548,109 da ke noma hekta 703,619 a tsakanin zango na hudu na shekarar 2020 da zangon farko na 2021 don bunkasa noman rani.

Ya ce, “jimillar kudaden zuwa karshen watan Fabrairu na 2021 sun kai tiriliyan N1.487 a karkashin shirye-shiryen noma daban-daban, wanda aka fitar da Naira biliyan 686.59 a karkashin tsarin kirkin Kasuwanci (CACS).

“Bankin ya kuma raba Naira biliyan 601.75 a karkashin shirin na ‘Anchor Borrowers Programm’ (ABP) ga manoma 3,038,649 don tallafawa samar da abinci da kuma rage matsalolin hauhawar farashin kayayyaki. A karkashin ‘Targeted Credit Facility’, bankin ya bayar da Naira biliyan 218.16 ga masu cin gajiyar 475,376, wanda kashi 34 na wadanda suka amfana da shirin SME ne.

“A karkashin tsarin zuba Jari na kasuwancin noma da tamakawa kanana da matsakaitan masana’antu (AGSMEIS), an bayar da Naira biliyan 111.62 ga masu cin gajiyar 28,961, wanda kashi 70 daga ciki suna bangaren noma ne.”

Gwamnan ya ce, bankin na CBN ya kuma samar da jari mai yawa ga cigaban matasa ta hanyar masana’antar kirkire-kirkire, a kokarin bunkasa samar da wutar lantarki gami da kudaden kiwon lafiya.

“A karkashin shirin Injiniyancin kirkirar masana’antu da kirkiro wanda aka fi mayar da hankali ga matasa, an raba Naira biliyan 3.19 ga masu cin gajiyar 341, wanda kashi 53 cikin 100 na masana’antar fim ne. A karkashin shirin ‘National Mass Metering Programme’, an raba Naira biliyan 33.45 ga kamfanoni guda tara domin sayen mitoci 605,852. An bayar da Naira biliyan 89.89 a karkashin Kamfanin Inganta kasuwar wutar Lantarki ta Nijeriya (NEMSF 2) ga kamfanonin rarraba kaya guda 11 don inganta masana’antar samar da wutar lantarki a Nijeriya. A karkashin Naira biliyan 100 na Kula da Kiwan Lafiya, bankin ya bayar da Naira biliyan 94.34, kuma a shirye yake ya fadada wurin zuwa ayyuka 85 a masana’antar hada magunguna. Yana da yawa don fadada layukan magunguna, samo MRI guda shida da sauran kayan aiki da habaka dakunan gwaje-gwaje da sauran ayyukan asibiti,” inji shi.

Emefiele ya ce, bankin koli ya kuma bayar da Naira biliyan 803.36 ga ayyuka 228 a sassan bangarori daban-daban na harkar kawance, hakar ma’adanai, samar da karafa da masana’antun kunshe a karkashin Naira Tiriliyan 1.0.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Samar Wa Manoma Ingantattun Iri – NASC

Next Post

Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 455 Duk Shekara Saboda Rashin Tsaftar Muhalli – Majalisar Dattawa

RelatedPosts

Kudade

Akwai Isassun Kudade Ga Masu Kasuwanci, Cewar CBN

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Babban bankin Nijeriya (CBN) ya kawar...

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

by Sulaiman Ibrahim
2 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad Ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce,...

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

by Sulaiman Ibrahim
2 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad Hukumar nan da ke yaki da...

Next Post
Majalisar Wakilai

Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 455 Duk Shekara Saboda Rashin Tsaftar Muhalli – Majalisar Dattawa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version