Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Mun Shiga Gagarumar Matsalar ‘Yan Wasa -Klopp

by
2 years ago
in WASANNI
1 min read
Klopp
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Abba Ibrahim Wada

Mai horar da kungiyar kwallon kafa Liverpool Jurgen Klopp, ya harzuka matuka da raunin dan wasan tsakiyar kungiyar Fabinho ya yin karawarsu da kungiyar Midtjylland karkashin wasannin cin kofin zakarun Turai da suka fafata a ranar Talatar data wuce.

Fabinho dan Brazil ya bi sahun dan wasan bayan kungiyar Virgil Van Dijk wanda yaji rauni a satin da suka buga 2-2 da Everton da Joel Matip dukkanninsu masu tsaron bayan Liverpool da ke ci gaba da jinya, wanda ke matsayin babban kalubale ga tsaron bayan kungiyar dai-dai lokacin da wasannin sabuwar kaka suka kankama.

Labarai Masu Nasaba

Ban Fitar Da Ran Bugawa Real Madrid Wasa Ba A Nan Gaba, Cewar Mbappe

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

A kalaman Jurgen Klopp bayan tashi daga wasan na ranar Talata da Liverpool ta yi nasara da kwallaye biyu da nema, ya ce sam raunin na Fabinho ba shi suka yi fata ba kuma sun shiga gagarumar matsalar ‘yan wasan baya.

ADVERTISEMENT

Kafin yanzu dai Klopp na amfani da Fabinho ne don cike gurbin Ban Dijk wanda ya samu rauni tun ranar 17 ga watan nan ya yin karawarsu da Everton hakan kuma na  nuna cewa raunin na Fabinho a yanzu zai sanya Klopp a tsaka mai wuya wajen laluben wanda zai cike gurbin ‘yan wasan biyu masu matukar amfani ga tawagar.

Yanzu haka dai matashin dan wasan na Liverpool mai shkearu 19 daya dawo daga aro, Rhys Williams ne zai hada karfi da Joe Gomez wajen rike bayan kungiyar har zuwa lokacin da manyan ‘yan wasan bayan zasu warke su koma fili.

Sai dai ko a bara mai koyarwa Jurgen Klopp ya koka da yadda ake yawan jikkata masa ‘yan wasa ba kuma tare da daukar mataki ba akai daga hukumomi wanda hakan yasa a halin yanzu yayi kira akan a sake saka ido akan yadda ake nunawa ‘yan wasan nasa keta.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan Wasan PSG Ta Faransa Sun Buga Wasa Cikin Dar-dar A Turkiyya

Next Post

Wasan Juventus Da Barcelona Ya Bar Tarihi Kala-kala

Labarai Masu Nasaba

Ban Fitar Da Ran Bugawa Real Madrid Wasa Ba A Nan Gaba, Cewar Mbappe

Ban Fitar Da Ran Bugawa Real Madrid Wasa Ba A Nan Gaba, Cewar Mbappe

by Abba Ibrahim Wada
22 hours ago
0

...

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

by
4 days ago
0

...

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
5 days ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
2 weeks ago
0

...

Next Post
Juventus

Wasan Juventus Da Barcelona Ya Bar Tarihi Kala-kala

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: