Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home WASANNI

Mun Yi Babban Kuskure A Wasan Porto – Ronaldo

by Sulaiman Ibrahim
March 11, 2021
in WASANNI
2 min read
Ronaldo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Juventus, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa kungiyar ta Juventus tayi babban kuskure na rashin nasarar da sukayi a wasan da suka buga da kungiyar kwallon kafa ta FC Porto a gasar cin kofin zakarun turai na bana.

FC Porto ta yi waje da Juventus a gasar Champions League, duk da rashin nasara da ta yi da ci 3-2 a Italiya a wasan da suka yi ranar Talata kuma kungiyoyin sun buga wasa na biyu a gasar cin kofin zakarun Turai don fayyace wadda za ta kai fafatawar wasan kusa dana kusa dana karshe.

Kungiyar ta Portugal ta ci wasan farko da suka yi a cikin watan Fabrairu da ci 2-1, ya yin da Juventus ta ci 3-2, jumulla Porto ta kai zagayen gaba ne, bayan da ta ci kwallo biyu a kasar ta Italiya.

“Bayan tashin daga fafatawar ne dan wasa Ronaldo ya bayyana cewa tabbas dashi da abokan wasansa sunyi babban kuskure a wasan da suka buga kuma hakan ya zama kamar darasi a tattare dasu”

Porto ta karasa fafatawar da ‘yan wasa 10 a cikin fili, bayan da aka bai wa Mehdi Taremi jan kati a minti na bakwai da komawa zagaye na biyu sannan wannan ne karon farko da Porto ta kai wannan mataki a Champions League, bayan da ta ci wasan farko, tun bayan shekara ta 2003 zuwa 2004 da ta yi nasara a kan Lyon.

A karo na biyar kenan ana cire Juventus a wasan zuwa daf da na kusa da na karshe a Champions League idan aka doke ta fafatawar farko wanda Juventus ta yi bajinta a biyar din shi ne karawa da Atletico Madrid, inda tasha kashi da ci 2-0 a Spaniya, ya yin da ta kai kuarter finals a Italiya, bayan da ta ci 3-0 a kakar wasa ta 2018 zuwa 2019.

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Ana Cece-kuce Kan Gayyatar Ahmad Musa Buga Wa Super Eagles Wasa

Next Post

Na Yi Bakin Cikin Rashin Fuskantar Barcelona – Neymar

RelatedPosts

Rohr

Muna Da Manyan ‘Yan Wasan Da Za Su Lashe Mana Kofin Afrika -Rohr

by Muhammad
17 hours ago
0

Kociyan tawagar Super Eagles ta Nijeriya, Gernot Rohr, ya bayyana...

Ahmad Musa

Me Ya Sa Ahmad Musa Ya Koma Kano Pillars?

by Muhammad
17 hours ago
0

Tuni aka kaddamar da kyaftindin tawagar kwallon kafar Super Eagels...

Turai

A Birnin Roma Za A Buga Wasan Karshe Na Kofin Nahiyar Turai

by Muhammad
17 hours ago
0

Hukumar kula da kwallon kafa ta nahiyar turai UEFA ta...

Next Post

Na Yi Bakin Cikin Rashin Fuskantar Barcelona – Neymar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version