Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Muna Tir Da Korar Ma’aikata Haka Siddan A Kaduna – ‘Yan Kwadago

by Sulaiman Ibrahim
April 8, 2021
in LABARAI
1 min read
Tallafin Gwamnatin Kaduna
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Shehu Yahaya, Kaduna

kungiyar kwadago ta kasa reshen Jihar Kaduna (NLC) ta nuna damuwarta dangane da Matakin da gwamnatin jihar ta dauka na  korar ma’aikatan kananan hukumomin jihar haka siddan.

kungiyar ta ce korar da gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamna el-Rufai tayi na  kori ma’aikatan ba bisa ka’ida inda tace ya sabawa hakkin bil-adama.

A wani taron manema labarai da kungiyar ta yi a Kaduna ta bayyana cewa korar ma’aikatan ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 wanda ya tanadi hanyoyin da ake bi wajen sallamar ma’aikata, da gwamnatin ta yi watsi da su.

Da yake gabatar da jawabinsa, shugaban kungiyar ta NLC kwamared Ayuba Suleiman, ya ce matakin da Gwamnatin Kaduna ta dauka na korar ma’aikata ta yi wa dokar kasa karan tsaye, inda ta kori ma’aikata sama da guda dubu ba tare da biyansu hakkokinsu ba da kuma bin dokokin tsarin daukar aiki da sallamar ma’aikaci.

Ayuba Suleiman, ya kara da cewa duk ci gaban da Gwamnatin Kaduna take ikirarin cewa ta samu, an samu nasarar ne bisa irin jajircewa da hazakar ma’aikata amma ta rufe idanunta ta kore su daga bakin aikin.
Shugaban ya yi tir da kakkausar murya wajen bayyana jimaminsu a kan korar ma’aikatan wanda da yawansu ma’aikata ne na kananan hukumomi.

A ranar Talata 6 ga wannan watan gwamnatin Jihar Kaduna ta bayar da sanarwa korar ma’aikata sama da guda dubu daga bakin aikinsu bisa abin da ta kira yi wa tsarin aikin gwamnati garambawul, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce daga galibin al’ummar jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Zulum Ya Jinjina Wa Yadda Sojoji Suka Fatattaki Boko Haram A Gwoza

Next Post

Dimukuradiyyar Cikin Gida A Jam’iyyu Zai Iya Magance Kashi 80 Na Matsalolin Zabe – INEC

RelatedPosts

INEC Ta Fara Horas Da Shugabannin Harkar Zaɓe Kan ƙara Yawan Rumfuna

INEC Ta Fara Horas Da Shugabannin Harkar Zaɓe Kan ƙara Yawan Rumfuna

by Sulaiman Ibrahim
44 mins ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kan ta...

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Isra'ila ta ce ta kai harin bama-bamai...

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Wani babban kwamandan ISWAP, Bukar Gana (wanda...

Next Post
Hukumar Zabe

Dimukuradiyyar Cikin Gida A Jam’iyyu Zai Iya Magance Kashi 80 Na Matsalolin Zabe – INEC

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version