Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Murtala Garo Jagora Ne Mai Kawo Cigban Al’ummarsa – Hon. Salisu Kabiru

by
1 year ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Hon. Salisu Kabiru
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Shugaban Karamar Hukumar Kabo, wanda kuma sh ne ya sake samun nasarar zabensa a karo na biyu, Hon. Salisu Kabiru Kabo ya bayyana godiyarsa ga Allah bisa amsa kira na yin tururuwa wajen fita zabe ba tare da samun tashin hankali ko korafi na rashin kawo kayan aiki ba, musamman. Ya bayyana haka ne a zantawarsa da ‘yan jarida a garin Kabo.

Ya ce, duba da irin abubuwa da Gwamnan Kano, Ganduje ya ke kawo wa na alkhairi a Kabo, kamar yanda sauran masu madafun iko na Karamar Hukumar suke yi, wadada suka hada da Kwamishinan Kananan Hukumomi, Alhaji Murtala Sule Garo, shi ya sa da wahala a ce wata jam’iyya ta yi tasiri,shi ya sa ba su da haufin samun nasara da APC ta yi a zaben.

Hon. Salisu Kabir Kabo ya ci gaba cewa, daga irin muhimman ayyuka da suka mora, akwai aikin tituna a sassa daban-daban, haka a harkar ruwan sha, ba su damMatsala, yanzu sun samar da rijiyoyin tuka-tuka da sanya sola guda 28 da za a iya jan ruwa na akalla mita 1,500 daga inda rijiyoyin suke. An yi gine-ginen makarantu da asibitoci, mutane shaida ne na abubuwan da Gwamna yake yi a Karamar Hukumar Kabo na bunkasa cigaban kasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Ya ce, wadannan abubuwa na ayyuka da ake yi su zai dora a kai bayan nasarar da ya sake samu ta lashe zaben shugabancin Karamar Hukumar Kabo a karo na Biyu, tunda mutane sun gamsu.

Daga nan sai Hon. Salisu ya yi kira ga al’umma su ci gaba da bada hadin-kai da suke bayarwa, da ci gaba da yi wa Gwamna da sauran jagorori addu’o’i nagari da bada goyon baya domin shugaba ya sami natsuwar da zai ci gaba da kawo wa al’umma romon damakwaradoyya.

Hon. Salisu Kabir ya jaddada goyon bayansu ga jagorancin Kwamishinan Kananan Hukumomi, wanda shi ne jigo a siyasar Karamar Hukumar Kabo, wanda duk wani aiki na ci gaban al’umma da gwamnati ta yi a yankin na Kabo, shi ne sanadi ko dai ta kai-tsaye, shi ne ya kawo ko kuma albarkacinsa aka yi, saboda haka ba su da wani abu da ya wuce yi masa fatan alkhairi, domin godiya da baki ta yi kadan sai dai kawai su fahimci me yake so kawai ya zama shi suke yi, domin duk abin da ake yi a Karamar Hukumar Kabo, shi ne jigo, duk abin da ya ce a yi, shi ake yi.

“Da Murtala Sule Garo zai ce a kama gudu daga nan Kabo zuwa Daura, kawai mutanen Kabo za su kama gudu ne, in sun je sannan za su ji mene ne ya faru, saboda sun san mutumin kirki ne kawai da yake kawo musu da alkhairi ko yaushe”, a cewar Shugaban Karamar Hukumar ta Kabo.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Burina Shine Wakilcin Da Zai Bunkasa Al’ummar Mazabata – Hon. Badau

Next Post

Sarkin Karaye Ya Jinjina Wa Kokarin Mataimakin Shugaban Jami’ar Wudil

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Sarkin Karaye

Sarkin Karaye Ya Jinjina Wa Kokarin Mataimakin Shugaban Jami'ar Wudil

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: