Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Musulmi Su Kara Azamar Tallafa Wa Marayu – Farfesa Tajoddin

by
1 year ago
in LABARAI
2 min read
Tallafa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Isa Abdullahi Gidan ‘Bakko,

An bukaci al’ummar musulmi da su kara azzama wajen tallafa wa marayu ta fuskoki da dama, ba lallai a lokutan watan azumi ba, duk lokacin da mutum ya fahimci marayan da ke kusa da shi, ya na bukatar tallafi, domin ya sami damar da gudanar da rayuwarsa, kamar yadda ma su iyaye ke yi.

Fitaccen malamin addininmusulunci kuma babban malami a cibiyar nazarin addinin musulunci da harshen larabci na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya mai suna Farofesa Tahir Tajoddin ya bayar da shawarar a lokacin day a amsa tambayoyin wakilinmu da ke Zariya kan muhimmancin tallafa wa marayu da kuma ire – iren tallafin da ya dace a rika yi wa marayu.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Farofesa Tahir ya ci gaba da cewar, musulunci bai ce sai a watan azumi ne kawai za a tallafa wa maraya ba, a cewarsa, ako wane lokaci, duk lokacin dad a maraya ke raye, ya na bukatar tallafin abububwanda zai yi amfani da su, domin inganta rayuwarsa nay au da kullun, kamar yadda duk wani mai rai ke bukata.

Game da ire – iren abubuwanda suka dace a rika tallafa wa marayu da su, a cewar shehin malamin sun hada da samar da abinci da abin shag a wadanda ke kula da maraya ko kuma marayun da kula da ilimin marayun da kuma kula da lafiyarsa, sai kuma tufafin da zai sa a jikinsa na yau da kullun, in har aka rungumi tallafa wa marayu da abubuwanda da aka ambata, babu ko shakka, maraya ko kuma marayu, ba za su rika tunanin sun rasa iyayensu ba, domin, kamar yadda Farofesa ya ce, bayan mutuwar mahaifinsa al’umma sun rungume  shi da hannu biyu.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, Farofesa Tajoddin ya tunatar da al’ummar musulmi das u rungumi tallafa wa marayu da dukiyarsu komi kankantar ta, kamar yadda ya ce, ba karamin lada wanda ya tallafa wa maraya ko marayu ke samu ba, a duk lokacin day a yi amfani da abin da ya mallaka ya tallafa wa maraya, a nan ne ya ce duk mai niyyar tallafa maraya ka day a dubi kankantar tallafin da zai bayar ko kuma yawan abin da zai bayar, abin bukata kawai shi ne, mutum ya tsarkake zuciyarsa ya bayar da tallafin domin Allah, ba domin al’umma su ce shi mutum ne mai tallafa wa marayu ba.

A dai zantawar da aka yi da Farofesa Tajoddin ya yi kira ga al’ummar musulmi da kuma kungiyoyin da aka kafa su domin tallafa wa marayu, da su mayar da hankalisu wajen samar da wata hanya ta koyar da marayu sana’o’in dogaro da kai da kuma iyayen marayun, wannan zai matukar tasiri, a cewarsa ga marayun da kuma ma su rikon marayun, su kasance ma su tallafa wa marayunsu da kuma kan su, ba ako wane lokaci, su na jirar  a ba su tallafi ba.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamna Buni Ya Bukaci Daukar Tsauraran Matakan Tsaro A Yobe

Next Post

Sarkin Karaye Ya Amince Da Nadin Abba Chiroma Sabon Dagacin Rimin Gado

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
6 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
8 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
16 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
18 hours ago
0

...

Next Post
Karaye

Sarkin Karaye Ya Amince Da Nadin Abba Chiroma Sabon Dagacin Rimin Gado

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: