Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home Uncategorized

Mutane 656 Ne Suka Kamu Da Cutar Kyanda A Jihar Kebbi

by Tayo Adelaja
September 25, 2017
in Uncategorized
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin-kebbi

Gwamnatin Jihar Kebbi ta tabbatar da faruwar matsalar kamuwa da cutar kyanda ga mutane 656 da ake zargi sun kamu da cutar a kananan hukumomi 21 da ke fadin jihar.

samndaads

Kwamishinan kiwon  lafiya ta Jihar Kebbi, Alhaji Usman Umar Kambaza, ya bayyana hakan ga  manema labarai a Birnin-Kebbi, cewa za a tura kungiyoyin masu yin allurar rigakafi guda dubu 1,131 don gudanar da allurar  rigakafi zagaye na biyu, domin a iya magance matsalar cutar kyanda a fadin jihar.

“Don magance wannan, jihar na shirin yakin  da cutar kyanda tare da goyon bayan Kungiyar Kula da kiwon Lafiya ta Kasa da sauran abokan hulda. Ana sa ran fara yaki da cutar kyanda  a ranar 26 ga watan Satumba, kuma kimanin yara dubu 898,174 ake sa ran za a yi wa allurar rigakafi a cikin jihar ta kebbi” in ji kwamishinan.

Bugu kari , Kambaza ya bayyana cewa za a ajiye masu bayar da allurar rigakafi a wurare daban-daban a bakin gidajen mutane a mazabu 225 da ke jihar, inda ya kara da cewa “babu wata mace da za ta yi tafiyar da ta wuce fiye da kilomita daya don yin wa ‘ya’yanta allurar rigakafi.”

Daga nan Kwamishinan ya bukaci ‘yan jarida, hakiman gargajiya da shugabannin addinai, da sauran masu ruwa da tsaki don shiga cikin shirin tattara mata da masu kula dasu domin kaucewa yaduwar cutar kyanda, saboda haka a fito a karbi allurar rigakafi.

A daya bangaren kuwa, Babban Sakataren hukumar kula da Kiwon Lafiyar Jama’a na karkara ‘KBSPHDA’, Dakta Manir Jega, wanda ya kwatanta wannan adadi na wadanda suka kamu da cutar kyanda a kananan hukumomin jihar kebbi da abu marar dadin ji. Ya ce yawancin wadanda suka kamu da cutar, hakan ya faru ne saboda kin amincewa da fitowa  don yin allurar  rigakafi.

Dakta Manir Jega ya bayyana hakan ne a cikin wata ganawa da ya yi da manema labarai a Birnin Kebbi, ya ce hukumarsa za ta tabbatar da cewa wannan matsalar ta bullar cutar kyanda ta faru ne sanadiyyar rashin fitowa da yara domin karbar allurar rigakafin a lokutan da ake ta yekuwar allurar rigakafi a shekarar 2016 da suka gudanar a cikin jihar ta kebbi.

Bugu da kari ya ce, “muna da matsalolin cutar kyanda guda 656 a cikin kananan hukumomi 21 da ke jihar, daga cikinsu akwai matsalar cutar ta kyanda 77 da aka tabbatar a cikin hukumomi 12 da kuma wadanda ke fama da cutar sankarau, amma hukumarsa ta yi iya kokarinta na ganin ta dakile matsalar ta hanyar bayar da magani da kuma allurar rigakafi, wanda yanzu haka sun warke kuma an sallame su,” in ji shi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kashi 70 Na Cututtukan Da Ke Addabar Mutane Ana Samu Ne Daga Cin Naman Dabbobi —Dakta Ba’abba

Next Post

Gidauniyar Bill Gates Za ta Samar Da Maganin Kanjamau Mai Araha

RelatedPosts

Gadagi

Yadda Muke Samun Rufin Asiri Ta Sana’ar Gadagi – Muhammadu Auwal  

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa, Muhammadu Auwal da aka fi sani...

Sheik Karibullah

Sheik Karibullah Ya Nada Alhaji Kabiru Sani Kwangila Khadimul Nabiyya A Taron Maulidin Gidansa

by Sulaiman Ibrahim
1 week ago
0

A ranar Lahadi ne aka gudanar da Maulidin Manzon Allah...

Buhari

Buhari Ya Yi Wa Sultan Ta’aziyyyar Rasuwar Dan Uwansa

by Sulaiman Ibrahim
1 week ago
0

Shugaba Muhammadu Buhari ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Abdulkadir Jeli...

Next Post

Gidauniyar Bill Gates Za ta Samar Da Maganin Kanjamau Mai Araha

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version