Mutanen Da Suka Mutu A Harin Ƙunar Baƙin-Wake A Wajen Bikin Aure Ya Ƙaru Zuwa 18 A Borno
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutanen Da Suka Mutu A Harin Ƙunar Baƙin-Wake A Wajen Bikin Aure Ya Ƙaru Zuwa 18 A Borno

byMuhammad
1 year ago
Borno

A wani rahoto da Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Borno, BOSEMA, ta fitar ta ce adadin wadanda suka mutu a sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai a garin Gwoza da ke Karamar Hukumar Gwoza a ranar Asabar zuwa yanzu ya kai mutum 18, inda aka tabbatar da mutum 19 kuma sun samu raunuka.

LEADERSHIP HAUSA ta ce jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, ASP Nahum Daso, a ranar Asabar ya tabbatar da mutuwar mutane 8 tare da wasu mutane 15 da suka samu raunuka a yayin harin kunar bakin waken.

  • Mutun 6 Sun Mutu Harin Ƙunar Ɓakin Wake a Borno
  • Boko Haram Sun Sace Wani Alkali Da Matarsa Tare Da Awon-Gaba Da Wasu Mutane A Borno

Kazalika, wani karin bayani da Darakta Janar na BOSEMA, Dr. Barkindo Saidu, ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a ranar Lahadin ya bayyana cewa adadin wadanda suka mutu a daren ranar Asabar ya kai 18, yayin da 19 da suka samu raunuka daban-daban inda yanzu haka suna jinya a asibitocin Maiduguri.

Dr. Saidu, ya ce akan idonsa, da misalin karfe 3 na yammacin ranar Asabar, bam na farko ya tashi a Gwoza, wanda wata ‘yar kunar bakin wake ta tayar da bam a wajen bikin aure.

Ya kara da cewa sama da mutane 30 ne abin ya shafa tare da raunuka daban-daban inda wasu kuma suka mutu nan take.

Dr. Saidu ya ce bayan ‘yan wasu mintoci, an sake samun fashewar wani abun fashewa a kusa da babban asibitin da ke garin.

A safiyar Lahadi, wata majiya daga BOSEMA da ta nemi bukaci a sakaya sunanta ta ce, adadin yawan mutanen suka mutu na iya zarce 18 idan aka yi la’akari da girman raunukan da suka samu.

A gefe guda kuma wata majiyar ta yi zargin cewa sama da gawar mutane 25 aka dauko daga wurare uku kafin sojoji su rufe hedikwatar karamar hukumar tare da sanya dokar hana fita da yammacin ranar Asabar.

Wakilinmu LEADERSHIP HAUSA ya ruwaito cewa, Gwoza na daya daga cikin kananan hukumomin da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kwace a baya inda suka ayyana ta a matsayin mallakin su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
“Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne”

"Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne"

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version