Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Nadin Kwamishinonin INEC: Wasu Sun Samu, Wasu Ta Leko Ta Koma 

by
10 months ago
in LABARAI
2 min read
Nadin Kwamishinonin INEC: Wasu Sun Samu, Wasu Ta Leko Ta Koma 
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

Majalisar Dattawa ta tantance tare da amincewa da nada wasu sabbin Kwamishinoni Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) guda biyar, yayin da kuma ta leko ta koma wa wasu sakamakon fatali da amincewa da nadinsu a da’irar shugabancin hukumar.

Daga cikin wadanda ta leko ta koma wa, akwai Misis Lauretta Onochie, ‘yar asalin Jihar Delta, wadda fadar shugaban kasa ta gabatar ga zauren, da ake ta ka-ce-na-ce a kanta saboda zargin ‘yar Jam’iyyar APC ce mai mulki, duk kuwa da cewa ta fito fili ta musanta hakan a yanzu. Haka kuma majalisar ta kuma jingine nadin Farfesa Sani Muhammad Adam daga arewa ta tsakiya har sai kwamitinta na INEC ya gama bincike a kansa.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Zauren ya sanar da hakan a takardar manema labarai mai dauke da sa hannun mai taimaka wa shugaban majalisar kan harkokin yada labarai, Mista Ezrel Tabiowo.

Sanarwar ta yi karin bayanin cewa tantancewa tare da nada kwamishinonin ta biyo bayan nazarin rahoton kwamitin majalisar ne a kan hukumar zabe.

Wadannan kwamishinonin da majalisar ta amince da nadinsu su ne:Farfesa Abdullahi Abdu Zuru (Arewa Maso Yamma), Farfesa Muhammad Sani Kallah (Katsina), Farfesa Kunle Cornelius Ajayi (Ekiti), Dakta Baba Bila (Arewa Maso Gabas), kana da Saidu Babura Ahmad (Jigawa).

Da yake mika rahotonsa, shugaban kwamitin, Sanata Kabiru Gaya, ya ce kwamitinsu ya samu takardun korafe-korafe da dama a kan nadin Misis Lauretta Onochie da Farfesa Sani Muhammad Adam, wanda hakan ya jawo daukar matakin yin fatali da batun.

Har ila yau, shugaban kwamitin, Sanata Gaya ya kara da cewa, korafe-korafen sun zargi Misis Lauretta da shiga harkokin siyasa tare da kasancewa mamba a jama’iyar siyasa.

Haka zalika, ya ce nada ta a matsayin shugabar INEC ya saba wa tsarin raba daidai na mukaman gwamnatin tarayya, wanda kuma yanzu haka akwai kwamishiniyar INEC, Barista Mary Agbamuce-Mbu, wadda ‘yar asalin jihar Delta ce da tuni majalisa ta amince da nadin ta.

A batu na daban kuma, Sanata Gaya ya ce kwamitin ya dauki wannan matakin ta hanyar dogara da sashi na 14, karamin sashi (3) na kundin tsarin mulki wajen kin bayar da shawarar amincewa da Misis Onochie.

Har ila yau, kwamitin ya bukaci zauren majalisar ya jingine batun amincewa da nada Farfesa Sani Muhammad Adam, har sai kwamitin ya kammala binciken da yake gudanarwa kan korafe-korafen da aka gabatar masa dangane da nadin nasa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Shugabanci A 2023: ‘Ohanaeze Ndigbo Ta Kara Dagula Wa Inyamurai Lissafi’

Next Post

Lokaci Ya Yi Da ‘Yan Arewa Za Su Farka Kan Koma-bayan Yankin – Galadanci

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
7 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
9 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
20 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
1 day ago
0

...

Next Post
Lokaci Ya Yi Da ‘Yan Arewa Za Su Farka Kan Koma-bayan Yankin – Galadanci

Lokaci Ya Yi Da ‘Yan Arewa Za Su Farka Kan Koma-bayan Yankin - Galadanci

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: