Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

NAF Ta Kara Fadada Ayyukan Yaki Da Ta’addanci A Katsina

by Muhammad
January 13, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Tsaro Nijeriya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad,

A ci gaba da kokarin inganta ayyukanta na yaki da ‘yan bindiga da sauran masu aikata ta’addanci a yankin Arewa maso Yammacin kasar nan, Rundunar sojojin saman Nijeriya (NAF), sun shirya kafa wani filin gudanar da ayyuka (FOB) a Funtua, Jihar Katsina.

samndaads

Wannan sanarwar ta fito ne daga hannun Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar, Air Vice Marshal Ibikunle Daramola, a inda yake cewa, an bayyana hakan ne a ranar, 7 ga Janairu 2021, ta hannun shugaban hafsan sojojin sama (CAS), Air Marshal Sadique Abubakar, yayin ziyarar dubawa zuwa inda FOB din take.

Shugaban, wanda ya samu rakiyar ziyarar tare da Shugabannin Sojojin sama masu jagorantar horarwar da kwamandan ayyuka na musamman da kuma wasu Shugabannin sansanoni da daraktoci daga hedikwatar NAF, Kuma dukkan su sun samu karbuwa a filin FOB din daga Sarkin maskan Katsina, Dakacin Funtua, Alhaji Idris Sambo, da kuma Shugaban gudanarwa na karamar hukumar Funtua, Alhaji Umar Mustapha, wadanda dukkansu suka nuna farin cikinsu da ci gaban.

Da yake zantawa da manema labarai bayan duba wurin, Air Marshal Abubakar ya bayyana cewa, NAF da ke aiki tare da ‘yan uwa maza da mata da sauran hukumomin tsaro, za ta cigaba da jajircewa ba tare da wata matsala ba don tabbatar da tsaro da lafiyar dukkanin ‘yan Nijeriya, a duk inda suke zaune. Ya kuma yi karin haske da cewa, sabon FOB din, idan aka kammala shi, zai rage lokacin mayar da martani na jirgin saman kai hari na NAF zuwa abubuwan gaggawa a yankin, ta haka zai kawo tsaro kusa ga mutane. Don haka ya nemi goyon baya da hadin kan mutanen yankin domin samun nasarar tashi daga aikin.

Yayin da yake bayyana cewa tsaro aiki ne na kowa da kowa wanda ke bukatar sa hannun dukkan ‘yan kasa, shugaban a takaice ya karfafa gwiwar dukkan mutane a yankunan da abin ya shafa da su samar da bayanan da suka dace wadanda zasu taimakawa hukumomin tsaro wajen tabbatar da kariyarsu. Air Marshal Abubakar, yayin da yake mika godiyar sa ga Gwamnatin jihar Katsina kan ware filin ga NAF, ya kuma umarci Daraktan ayyuka da masu tallafawa NAF da su fara aiki ba tare da Bata lokaci ba, zuwa ga kammala aikin cikin sauri.

SendShareTweetShare
Previous Post

Shirin Zamanantar Da Cinikin Lemon Fata Ya Kusa Kankama A Kano – Na’alto

Next Post

Makaho Ya Sanya Kansa A Makarantar Koyon Tukin Jirgin Sama

RelatedPosts

Ebonyi

Kwamishinan ’Yan Sandan Ebonyi Ya Kama Hadiman Gwamnan Jihar Biyu Da Shugaban Karamar Hukuma

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rundunar 'yan sanda ta kama wasu...

Direbobi

Bakwai Sun Mutu Da Yawa Sun Jikkata A Rikicin Shugabancin Kungiyar Direbobi

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A kalla mutane bakwai ne suka...

Takalmi

Mata Ta Rafka Wa Mijinta Tsinin Dunduniyar Takalmi Ya Mutu

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Wata mata da ba a bayyana...

Next Post
Jirgin Sama

Makaho Ya Sanya Kansa A Makarantar Koyon Tukin Jirgin Sama

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version