Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

NAF Ta Raba Karin Tukunyar Iskar Shaka Ga Cibiyoyin Kebe Masu Korona

by Muhammad
January 13, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Tukunyar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad,

A wani bangare na gudummawar da ta ke bayarwa ga kokarin Gwamnatin tarayya na kula da annobar korona a karo na biyu, Rundunar Sojin Saman Nijeriya (NAF) a ranar, 7 ga Janairu 2021, ta raba karin tukunyar iskar shaka ‘Likuid Odygen’ (LOD) kyauta zuwa asibitoci da wuraren kebewa masu cutar, a Abuja.

samndaads

Wannan sanarwar ta fito ne daga hannun Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar, Air Bice Marshal Ibikunle Daramola, a inda yake cewa, sabbin wadanda suka ci gajiyar wannan karin rukunin sun hada da asibitin koyarwa na Jami’ar Abuja, Gwagwalada da kuma sashin Kula da ayyukan gwamnati a Abuja, wadanda suka ci gajiyar rukunin farko da aka raba a watan Satumbar 2020.

Tukunyar iskan, wanda kamfanin ‘NAF LOD Plant’ ta samar a rukunin ‘103 Strike Group’ (103 STG) da ke Yola, an matsar dasu zuwa ‘NAF C-130 Hercules’ ne, kuma aka dauke shi zuwa Filin jirgin sama na kasa da kasa na Nnmadi Azikiwe, Abuja kuma an mika shi ga wadanda suka amfana daga hannun kwamandan ma’aikatar lafiya (CMS), Air Commodore Gideon Bako, wanda kwamandan asibitin 063 na NAF Abuja ya wakilta, Group Captain Muzzammil Muhammed.

A nasa bangaren, daraktan sashin kiwon lafiya na asibitin koyarwa na jami’ar Abuja, Mista Nathan Yatufate, wanda ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar shirin, ya nuna jin dadinsa da wannan karramawar da NAF din ta yi, yana mai cewa, iskar shakar ta taimaka sosai wajen ceton rayukan masu cutar da dama a cikin ‘yan kwanakin nan.

A halin yanzu, NAF, a ranar 6 ga Janairu 2021 ta ba da silinda na LOD zuwa babban asibitin gundumar Maitama, Abuja don kula da marasa lafiya na korona. Shugabannin asibitin sun godewa NAF saboda samar da iskar, wanda a cewarsu, har yanzu shine abu mafi muhimmanci da ake bukata wajen kula da marasa lafiya masu cutar korna a asibitin.

SendShareTweetShare
Previous Post

NAF Ta Kai Ziyarar Ta’aziya Ga Dangin Marigayi Air Marshal Nsikak Eduok

Next Post

An Cafke Dan Nijeriya Bisa Mutuwar Wata Lauya A Nairobi

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Nairobi

An Cafke Dan Nijeriya Bisa Mutuwar Wata Lauya A Nairobi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version