Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Naira Na Shirin Sake Faduwa Warwas – FMDQ

by Muhammad
March 8, 2021
in LABARAI
2 min read
Kungiyar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
  • Za Ta Iya Kai Wa Dala 500 Cikin Mako Mai Zuwa

Daga Mahdi M. Muhammad,

Hukumar Kula da Dillancin Kasuwannin Kudi a Nijeriya (FMDQ) ta bayyana cewa, duk da hauhawar farashin danyen mai a wannan makon, dorewar bukatar Dala a kasuwar canjin kudade na waje yana nufin kudin Nijeriya na iya hawa a karshen mako da kashi 0.18 cikin rauni.

Bayanai daga hukumar ya nuna cewa, cinikin kudin waje a hukumance ya nuna cewa, an yi musayar Naira da Dala akan Naira 411, idan aka kwatanta da Naira 409.20 da aka rufe a ranar Litinin 1 ga Maris, 2021.

Darajar canjin ranar Juma’a kuma tana wakiltar Naira 4.5 ko 1.10 cikin 100 na faduwar darajar daga Naira 406.50 a ranar Alhamis 4 ga Maris. A zahiri, a ranar Juma’a, darajar Naira ta yi sama a farashin da yakai N415 a Dala daya.

A kasuwar da ba ta hukuma ba, bayanai sun nuna cewa, kudin cikin gida ba su canjawa a Dala 480/1 a cikin mako, amma yana iya canjawa a mako mai zuwa.

Canje-canjen na ‘Fored’ a hannun jari da masu fitar da kaya (I&E) duk da haka ya karu da kashi 25.29 bisa dari, tare da dala miliyan 83.93 da aka rubuta ranar Juma’a sabanin dala miliyan 66.99 da aka saka ranar Alhamis.

Rahotanni a shafin yanar gizo na CBN ya nuna cewa asusun ajiyar Nijeriya na waje, wanda ya baiwa babban bankin kasar tsokar kare Naira, ya ragu da dala miliyan 184.5 zuwa dala biliyan 34.91 kamar yadda yake a ranar 3 ga Maris, 2021, idan aka kwatanta da dala biliyan 35.09 kamar yadda yake a ranar 26 ga Fabrairu, 2021, lokacin an rage darajar Naira.

A cikin Fabrairu 1 zuwa 26 kadai an samu raguwar ajiyar waje ya kusan dala Biliyan 1.1. Ragowar adadin ya nuna cewa, CBN na yin duk abin da zai iya don biyan bukatar karin dala daga masana’antu da ‘yan kasuwa don nisanta su da kasuwar da ke daidai da kuma dakatar da sayayyar musayar kudaden waje.

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Godwin Emefiele, a kwanan baya ya jaddada bukatar da ke akwai na hana babbar raguwar ajiyar waje ta hanyar inganta samar da kayayyakin da ake shigo da su cikin gida.

Amma ya lura cewa kasar tana da isassun kudaden da zata dauki nauyin watanni bakwai masu zuwa na shigo da kayayyaki kuma ba bukatar firgita.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Bauchi Na Shirin Raba Tsaftacaccen Ruwa Sha Lita Miliyan 75 Kullum

Next Post

Zulum Ya Bankado ’Yan Hijira 650 Na Bogi

RelatedPosts

Malamai

Kungiyar Malamai Ta Tallafa Wa ‘Yan Hijira Sun Shirya Taron Bita Na Ramadan

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Kungiyar Hada Kan zauran Malamai da kungiyar...

Zakzaky

Ramadan: El-Zakzaky Ya Raba Tallafin Abinci Ga Mabukata

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Shugaban harkar musulunci a Nijeriya (IMN)...

Musulmi

Wajibi Ne Musulmi Su Ajiye Bambancin Akida Dan Hadin Kai Da Samun Zaman Lafiya – Shareef Ishak  

by Muhammad
1 hour ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, An bayyana cewar wajibi ne musulmi...

Next Post
Hijira

Zulum Ya Bankado ’Yan Hijira 650 Na Bogi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version