CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Najeriya Ta Ci Gajiyar Hadin Gwiwar Da Ake Yi Tsakanin Sin Da Afirka

by CRI Hausa
November 28, 2020
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Najeriya Ta Ci Gajiyar Hadin Gwiwar Da Ake Yi Tsakanin Sin Da Afirka

DCIM100MEDIADJI_0150.JPG

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Jiya ranar 27 ga wata, an kaddamar da cibiyar horo ta Luban ta kasar Sin a Najeriya, da nufin ba da horon dabarun fasaha domin taimakawa daliban kwaleji cimma bukatun kasuwa. Cibiyar wadda jami’ar Abuja ta karbi bakuncinta, za ta fara ne a matakin farko da kwasa-kwasan da suka hada da kula da zirga-zirgar jiragen kasa da gadoji da ramukan jiragen kasa.

Wannan cibiyar horo ta Luban yana daya daga cikin cibiyoyin horo na Luban guda goma da kasar Sin ta shirya kafa su a kasashen Afirka a karkashin inuwar dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka ta FOCAC, wanda ta sanar a watan Satumban shekarar 2018, a kokarin koyarwa matasan Afirka fasahohin sana’o’i.
Dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka ta FOCAC da aka kafa a shekarar 2000 wani muhimmin dandali ne da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka guda 54 wajen hadin gwiwarsu ta a zo a gani, kana wani sabon tsari ne da ya martaba ka’idar kasancewar bangarori daban daban da ma hadin kan kasa da kasa. A cikin shekaru 20 da suka gabata, Sin na bin dabarar “cimma muradu da kuma martaba ka’idoji” da ma dukufa wajen hadin kan bangarorin biyu don samun nasara da bunkasuwa tare.
Sakamakon da aka samu a karkashin inuwar FOCAC ya amfani kasashen Afirka daban daban. Alal misali, Tarayyar Najeriya ta ci gajiyar dandalin FOCAC sosai. A cikin wadannan shekarun baya, Najeriya ita ce wadda ta fi samun yawan kwangilolin gini da samun kayayyakin kasar Sin a nahiyar Afirka, kana ta zama abokiyar cinikayyar Sin mafi girma ta biyu a Afirka. A shekarar 2019, jimillar cinikayya a tsakanin Sin da Najeriya ta zarce dala biliyan 19.2, wadda ta karu da kaso 26.3 bisa ta shekarar 2018, saurin karuwar jimillar ya zama na farko a cikin muhimman abokan cinikayyar Sin guda 40. Bugu da kari kuma, hanyoyin dogo a tsakanin Abuja zuwa Kaduna da tsakanin Lagos zuwa Ibadan da cikin Abuja, tashar samar da wutar lantarki mai aiki da karfin ruwa ta Zungeru, tashar jiragen ruwa ta Lekki, yankin cinikayya marasa shinge ta Guangdong da ke Ogun, yankin ciniki cikin ’yanci na Lekki da kasar Sin ta gina sun aza harsashi mai inganci ga ci gaban masana’antun Najeriya. Ban da wannan kuma, cudanyar al’adu a tsakanin bangarorin biyu ta kara bunkasuwa, inda yawan daliban Najeriya da ke karatu a kasar Sin ya kai 6800 a shekarar bara, adadin da ya zama na farko a Afirka.
Hakikanan abubuwa sun shaida cewa, an samu sakamakon a zo a gani a karkashin inuwar FOCAC, wanda ya kawo wa jama’ar Sin da Afirka alheri sosai. Hadin kai a tsakanin bangarorin biyu ya taimaka wa farfadowar al’ummar Sin, yayin da ya kara azama ga ci gaban Afirka bisa karfin kansu. Lamarin kuwa ya shaida cewa, kasashe masu tasowa na iya samun wata hanyar farfardowa da ta dace da yanayinsu bisa karfin da suke da shi. (Marubuciya: Kande Gao)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Xi Ya Taya Murnar Kammala Gwajin Jirgin Ruwan Fendouzhe Mai Nutso Cikin Teku

Next Post

Za A Shigar Da Tsaffin Ma’aikatan N-power Cikin Tallafin Babban Bankin Nijeriya

RelatedPosts

Wane Irin Tsarin Cudanyar Tattalin Arzikin Duniya Ake Bukata?

Wane Irin Tsarin Cudanyar Tattalin Arzikin Duniya Ake Bukata?

by CRI Hausa
17 hours ago
0

A cikin ‘yan watannin da suka gabata, wasu mutane sun...

Xi Ya Saurari Rahoton Aikin Gwamnatin Yankunan Hong Kong Da Macao

Xi Ya Saurari Rahoton Aikin Gwamnatin Yankunan Hong Kong Da Macao

by CRI Hausa
17 hours ago
0

A yau ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya saurari...

Jiangxi: An Taimakawa Mutane Wajen Saukaka Begen Gida Da Suke Yi Ta Kafar Bidiyo Kai Tsaye

Jiangxi: An Taimakawa Mutane Wajen Saukaka Begen Gida Da Suke Yi Ta Kafar Bidiyo Kai Tsaye

by CRI Hausa
17 hours ago
0

A kauyen Huikeng a garin Xinwan na gundumar Xiushui a...

Next Post
Shirin N-Power

Za A Shigar Da Tsaffin Ma'aikatan N-power Cikin Tallafin Babban Bankin Nijeriya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version