Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home ILIMI

NANS Ta Yi Kira Ga Gwamnati Da Kungiyar Malamai Kan Yajin Aikin Jami’o’i

by Tayo Adelaja
September 15, 2017
in ILIMI, RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

Kungiyar dalibai ta kasa NANS ta yi kiga ga gwamnatin tarayya da kungiyoyin malamai da su zauna tuburin sulhu domin shawo kan matsalar yajin aikin da malaman jami’o’i ke ci gaba da yi a halin yanzu. Mataimakin shugaban kungiyar dalibai ta kasa Kwamared Shattima Umar ne yayi wannan kiran a wani taron manema labaru da ya Kira kan bahasin babban taron da suka yi a Bauchi kan tattalin arziki, tsaro da kuma ci gaban kasa a kwanakin baya.

samndaads

Ya ci gaba da cewa “NANS tana kira ga gwamnatin tarayya da malamai da su zauna waje goda domin ganin an kawo karshen wannan yajin aikin da ake ta fama da shi. Domin dalibai suna gida alhali daf wasu zasu fara jarabawa kuma sai ga shi malamai sun zunduma yajin aiki. Muna kira ga gwamnati da malamanmu da su taimaka mana mu dalibai su dawo su sasanta domin ilimi ya ci gaba da tafiya yanda ya kamata a kasar nan”. In ji shugaban NANS

Shatti Umar ya kuma jinjina wa kokarin da gwamnatin tarayya take yi wajen inganta tsaro a makarantu sai ya bukaci gwamnati da ta kara himma domin daliban su kasance masu samun amince a lokacin da suke ajujuwan daukan darasin nasu.

Ya kara da cewa “Muna jinjina wa majalisar tarayyar Nijeriya a bisa kawo kudirin da zai bai wa matasa damar shiga takarar siyasa. Muna kira ga shugaban Nijeriya da ya sa hanu kan wannan kudirin domin matasa su ma a dama da su wajen shugabacin kasar nan”. In ji Shattima

Kwamared Umar Shattiman ya kuma jinjina wa gudummowar da gwamnatin jihar Bauchi ta ba su wajen tallafa musu kan babban taron da suka gudanar a Bauchin “muna godiya wa gwamnan jihar Bauchi kan tsayawa da yake yi kan tallafa wa dalibai a kowane bangare, muna kuma kira ga sauran gwamnoni da su yi koyi da irin halin gwamnan jihar ta Bauchi kan tallafa wa dalibai”.

Mukadashin Shugaban kungiyar dalibai ta kasa ya ce kimanin daliban sama da miliyan 41 ne suke karkashin shugabancinsu, don haka, da bukatar gwamnati ta yi la’akari da yawansu domin shigar da su cikin al’amurar rayuwa, domin wasu daga cikinsu Allah ya yi musu  baiwar tafiyar da al’amurar mulki, da siyasa da sauransu

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Aikin Hanya A Kauru

Next Post

BABBAN LABARI: ‘Da Naira 1,000 ‘Yan Fashi Ke Yaudarar Matasan Rijana’

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
2 days ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post

BABBAN LABARI: ‘Da Naira 1,000 ‘Yan Fashi Ke Yaudarar Matasan Rijana’

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version