Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Napoli Ta Nada Gattuso A Matsayin Sabon Koci

by
2 years ago
in WASANNI
1 min read
Gattuso Ya Karbi Horas Da Kungiyar Napoli

FILE PHOTO: Soccer Football - Serie A - Parma v AC Milan - Stadio Ennio Tardini, Parma, Italy - April 20, 2019 AC Milan coach Gennaro Gattuso before the match REUTERS/Jennifer Lorenzini

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kungiyar kwallon kafa ta Napoli ta nada tsohon kociyan AC Milan, Gennaro Gattuso, a matsayin sabon kociyanta bayan korar Carlo Ancelotti da ta yi a ranar Talata sa’o’i bayan nasarar da ya samu kan kungiyar Genk da ci 4-0 wanda ya bai wa Napolin damar tsallakawa zagaye na gaba a gasar cin kofin zakarun turai na Champions League.

Gattuso mai shekara 41, shi ne tsohon kociyan AC Milan kuma ya bar kungiyar ne a karshen kakar wasanni ta bara sakamakon rashin tabuka abin azo a gani wanda yasan kungiyar ta kare a mataki na tara.

Napoli dai na matsayi na bakwai ne a yanzu a gasar Siriya A da maki takwas tsakaninta da kungiyar da ke matsayi na hudu a jadawali wanda hakan yake nufin idan aka cigaba da tafiya a haka ba zata samu damar zuwa kofin zakarun turai ba

Labarai Masu Nasaba

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Chiellini Ya Bar Juventus

“Akwai bukatar mu zage dantse mu yi aiki da kyau domin ganin mun samu nasara a wannan lokacin saboda ba kawai mai koyarwa bane yake aiki domin a samu nasara suma ‘yan wasa da shugabanni tare da magoya baya duka sai sunyi aiki da gaske” In ji Gattuso.

ADVERTISEMENT

Manufar dauko sabon kociyan dai a yanzu ita ce, dawo da makin da kungiyar ta yi asara a baya domin komawa gasar Zakarun Turai a shekara mai zuwa wanda kuma shugaban kungiyar, yake ganin Gattuso zai iya wannan aiki.

Gattuso ya buga kwallo karkashin koyarwar Ancelloti a AC Milan ya kuma ce, kamar mahaifi yake a wajensa kuma da shakuwa sosai kuma yana taimaka masa sannan a cewar Gattuso Ancelotti ya samu dukkan nasara kuma shima yana bukatar aiki sosai domin samun irinta a rayuwa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Watakila Anthony Joshua Ya Fafata Dambe A Nijeriya

Next Post

Inason Kafa Irin Tarihin Messi —Ansu Fati

Labarai Masu Nasaba

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

by
1 day ago
0

...

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post

Inason Kafa Irin Tarihin Messi ---Ansu Fati

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: