Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Nasarawa Ta Yi Sabon Kwamishinan ’Yan Sanda

by Tayo Adelaja
September 21, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela, Damaturu

Sabon kwamishinan ‘yansanda Jihar Nasarawa Mohammed Uba Kura ya isa jihar tare da soma aiki nan take.

samndaads

Kwamishinan wanda ya samu marhabin jami’an ‘yansanda da yin faretin musamman a hedikwatar rundunar ‘yansanda da ke Lafia, ya fara aiki ne ta hanyar ganawa da manyan jami’an ‘yansanda a ofishinsa.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan da kammala ganawarsa da manyan jami’an rundunar a jihar, sabon kwamishinan ya ce zai mayar da hankali ne kan yaki da manyan laifuka da ci gaba da tabbattar da kyakkyawar zaman lafiya a jihar.

Haka nan ya ce, shi da kansa zai kasance mai rangadi yana sanya ido a aikin jami’an domin tabbattar ba su wucce gona da iri.

Da yake yaba wa Sufeto Janar na ‘yansanda kan nada mukamin Kwamishinan ‘Yansanda Jihar Nasarawa, Kura ya yi kira ga mazauna jihar da su rinka bai wa jami’an tsaro hadin kai game da aikinsu na dakile muggan ayyuka da tabbattar da kyakkyawar zaman lafiyar al’umma.

A cewarsa, “Ko da kana dan jarida, ko dan siyasa, ko basaraken gargajiya da sauransu, ka kalli kanka a matsayin dansanda ta hanyar sa ido da samar da bayanan da za su taimaka wa ‘yansanda yaki da muggan ayyuka”.

Ya kara da cewa, “Idan ka ga ana aikata muggan ayyuka, ko da ba za ka iya zuwa kai tsaye ka fada min ko wani jami’i ba, kana iya sanar wa shugabanni da kake kusa da su, su kuma su sanar da mu domin daukar matakin da ya dace”.

Kafin nada shi kwamishinan ‘yansanda Jihar Nasarawa, Kwamishina Mohammed Uba Kura shi ne kwamandan kwallejin koyar da dabarun bincike na ‘yansanda da ke Enugu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Daliban Kwalejin Ilimi Ta Yobe 400 Sun Yi Rijista Da TRCN

Next Post

Kungiyar Matasan Funtuwa Ta Caccaki Wakilcin Sanata Abu Ibrahim

RelatedPosts

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

by Yahuzajere
9 hours ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) da...

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

by Sulaiman Ibrahim
15 hours ago
0

Gwamna jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal Ya sanar da Mutuwar...

Sakatariyar

Sakatariyar Karamar Hukumar Da Ake Wata Guda Ba A Shige Ta Ba A Kano

by Muhammad
23 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kananan Hukumomi ne ke zaman gimshikai...

Next Post

Kungiyar Matasan Funtuwa Ta Caccaki Wakilcin Sanata Abu Ibrahim

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version