Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

NASRDA Ke Da Hakkin Kaddamar Da Tauraron Dan Adam A Nijeriya – Buhari  

by
11 months ago
in LABARAI
2 min read
NASRDA
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya sake jaddada cewa hukumar gudanar da binciken sararin samaniya ta kasa (NASRDA) ita kadai ce hukumar da take da alhakin gudanar da bincike tare da kaddamar da tauraron dan Adam a Nijeriya.

Shugaban kasa ya bayyana hakan a babban taron da hukumar ta gudanar na kasa (NSC) a birnin Abuja, yayin da Buhari ya yi cikakken bayani dangane da ci gaban da ake dashi a kimiyya da fasaha, musamman abinda ya shafi gudanar da bincike, sadarwa, tare da kaddamar da tauraron dan Adam, aiki ne wanda ya kebanta da hukumar kula da sararin samaniya ta kasa. Har wala yau shugaban kasa ya bukaci shugaban hukumar hadi da ilahirin ma’aikatan hukumar su yi aiki da dokar NASRDA ta 2010.

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Haka zalika kuma shugaban kasa ya yaba da kokarin hukumar NASRDA bisa nasarorin da ta samu a fannin kimiyya da fasaha a Afrika. Ya ce hukumar binciken sararin samaniyar ta taka muhimmiyar gudumawa wajen nuna kwarewa ta hanyar zayyana wa, ginawa tare da dora tauraron dan Adam a Nijeriya. Wadanda ya bayyana sun hada da NigeriaSat -1, NigeriaSat–2, NigComSat-1R tare da babban hobbasar kaddamar da tauraron NigeriaSat-D, wanda injiniyoyin Nijeriya suka zayyana tare da kera shi. Al’amarin da shugaba Buhari ya bayyana a matsayin nasara tare da sauya fasalin ci gaban Nijeriya a fuskar kimiyya da fasaha.

A nashi bangaren, Darakta Janar a hukumar NASRDA, Dr Halilu Shaba, ya yi karin haske dangane da tauraron dan Adam, samfurin NigeriaSat-2, wanda ya sanar da cewa har yanzu yana ci gaba da gudanar da aiki kamar yadda ya dace kuma ya na bayar da ingantattun bayanan da ake bukata bisa yadda aka tsara.

A hannu guda kuma, shugaban hukumar NASRDA ya yi karin haske dangane da ci gaban da suke samu tare da kudurin su na gina wa da kaddamar da karin sabbin tauraron dan Adam guda biyu, samfurin Synthetic Aperture Radar (Nigeria SAR -1) ta Optical Earth Observation Satellite (NigeriaSat-3).

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Dole Sai Nijeriya Ta Cire Tallafin Fetur Za A Samu Ci Gaba – Ministan Mai

Next Post

Magidanci Ya Halaka Matarsa Da Duka Kan Hana Shi Rancen Naira 2,000 A Edo

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
4 hours ago
0

...

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

by
8 hours ago
0

...

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

by
9 hours ago
0

...

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

by
10 hours ago
0

...

Next Post
Magidanci Ya Halaka Matarsa Da Duka Kan Hana Shi Rancen Naira 2,000 A Edo

Magidanci Ya Halaka Matarsa Da Duka Kan Hana Shi Rancen Naira 2,000 A Edo

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: