Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASASHEN WAJE

NATO Za Ta Yaki IS A Syria Da Iraki

by Tayo Adelaja
September 30, 2017
in KASASHEN WAJE
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kungiyar tsaro ta NATO za ta shiga yakin da Amurka ke jagoranmta akan Mayakan IS, a Syria da Iraki. Matakin na zuwa kafin ganawar da shugaban Amurka Donald Trump zai yi da shugabannin mambobin kungiyar NATO a Brussels  ranar Alhamis. Wasu majiyoyin Difolamsiyya ne suka tabbatar da cewa NATO za ta shiga yakin da Amurka ke jagoranta akan mayakan IS, bayan Trump ya bukaci kungiyar tsaron ta mayar da hankali ga yakar ayyukan ta’addanci.

Tuni sakararen harakokin wajen Amurka Red Tillerson ya bayyana fatan ganin NATO ta shigo cikin yakin da Amurka ta kaddamar akan IS duk da wasu mambobin kungiyar na dari-dari da abkawa cikin wani yaki a yanzu. Wasu majiyoyi daga Turai sun ce Faransa da Jamus sun amince da kudirin na Amurka kan shigowar NATO a yakin a ganawar da Trump zai yi da shugabannin kasashen na Turai

samndaads

Rahotanni sun ce Jakadun kasashen mambobin NATO sun tsara matakan yaki da ta’addanci a taron da shugabannin na Turai za su yi da Donald Trump. Matakan kuma sun hada da fadada ayyukan jiragen leken asiri na NATO wajen yakar IS a Syria da Iraki. Wani labara mai kama da wannnan kuma, a ci gaba da samun koma baya da kungiyar IS din ke yi, Amurka ta ce ta yi barin wuta kan kungiyar ta’addancin, wanda ya hallaka da dama daga cikin mabiyanta a kasar Libiya.

Wasu hare-haren jiragen sama da Amurka ta kai a kasar Libiya sun hallaka karin mayakan IS, wanda wannan shi ne karo na biyu da Amurka ta kai irin wadannan hare-haren a wannan kasa ta arewacin Afirka ciki kasa da mako guda, tare da hadin gwiwar gwamnatin hadin kan kasar Libiya ta GNA, sojojin Amurka sun kai hare-haren jiragen sama da aka auna kan ‘yan IS ranar Talata, inda mayakan IS din da dama su ka mutu, a cewar Rundunar Sojin Amurka mai kula da aiyukkan soji a Afirka, a wata takardar bayani da ta fitar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Faransa Za Ta Taimaka A Magance Rikicin Iraki

Next Post

An Ta Da Bam A Masallacin ’Yan Shia A Kabul

RelatedPosts

Faduwar Trump

Me Zai Biyo Bayan Darewar Karajar Biden Da Faduwar Trump?

by Muhammad
2 days ago
0

Idanun duniya na kan ranar Larabar jiya, 20 ga Janarairu,...

Allurar Korona

An Soma Yin Allurar Korona A India Da Brazil

by Muhammad
2 days ago
0

A yau asabar kasashen Duniya da suka hada Indiya ,Brazil...

Trump Ya Fice Daga Fadar ‘White House’ Gabanin Rantsar Da Biden

Trump Ya Fice Daga Fadar ‘White House’ Gabanin Rantsar Da Biden

by Muhammad
3 days ago
0

Trump ya ce mutane "ba su san aiki tukuru" da...

Next Post

An Ta Da Bam A Masallacin ’Yan Shia A Kabul

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version