Nazari Kan Bunkasuwar Sin Bisa Yadda Aka Fitar Da Al’ummar Jino Daga Kangin Talauci
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Bunkasuwar Sin Bisa Yadda Aka Fitar Da Al’ummar Jino Daga Kangin Talauci

byCGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Nazari

Kwanan baya, na kai ziyara kauyen Bapo, kauye ne na al’ummar kabilar Jino da da ke yankin Xishuangbanna na lardin Yunnan dake kudu masu yammacin Sin, inda na ga an rataya hoton tsohon shugaban kasar Sin marigayi Mao Zedong a kofar gidajen mazauna kauyen, kuma Miko wadda ke rayuwa a kauyen ta fada min cewa, dalilin hakan shi ne don bayyana godiya da amincewarsu ga gwamnatin Sin.

 

Ta ce, a watan Oktoba na shekarar 1952 bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, gwamnatin kasar Sin ta tura tawagogin aiki zuwa sassan dake fama da matukar talauci da ke karkarar lardin Yunnan. Ma’aikatan tawagogin sun yi rayuwa da aiki tare da mazauna wuri, sun yi ayyuka da suka hada da gina madatsar ruwa da gidaje, da aikin debo ruwa da daka shimkafa, kana sun taimakawa al’ummar wuri a mabambantan harkoki, wanda hakan ya sa al’ummar Jino suka fita daga zamantakewar al’umma irin ta zamanin da da can.

  • Waƙa Sana’a Ce Sai Da Ilimi Da Jari -Wizzamany
  • Jihar Filato Ta Yi Hadaka Da Kasar Bulgeriya A Fannin Noma

A halin yanzu, iri wadannan tawagogi na ci gaba da aikinsu a tsaunuka dake Xishuangbanna, kuma ma’aikatan sun gaji ruhi daga tsoffinsu, suna kokarin fitar da hanyoyi mafiya dacewa na farfado da kauyuka da raya sana’o’in wurin. Har ma mazauna wuri su kan ce, yadda ba za a bar gishiri a rayuwa ba, hakan nan ma ba za a bar tawagogin ba.

 

Miko ta ce, a da zaman rayuwar al’ummar Jino ya godara ne kan aikin farauta, kuma al’ummar Jino suna shuka ganyen shayi don biyan bukatunsu ne kawai. Amma daga baya gwamnatin wurin ta yi amfani da fifikon da al’ummar Jino ke da shi don kyautata zaman rayuwarsu, inda ta gabatar da tsarin “Kauye daya haja daya”, don raya tattalin arzikin wurin.

 

Misali kauyen Bapo da na ziyarta, na dogaro da al’adun ‘yan kabilar Jino masu ban sha’awa, da ma ganyen shayi na Pu’er mai inganci, abin da ya sa ya zama kauyen da ya shahara a bangaren yawon shakatawa bisa al’adunsa a Yunnan.

 

A shekarar 2019, al’ummar Jino sun fita daga kangin talauci gaba daya. Miko ta gaya min cewa, a yanzu tsoffin gidaje dake cikin tsauni sun kasance wani sashi na bayyana al’adun Jino, bayan mutanen da a baya ke rayuwa cikinsu sun kaura zuwa gidaje na zamani.

 

Daga zamantakewar al’umma irin ta zamanin da da can, zuwa samun bunkasuwa irin ta zamani, daga gidaje marasa inganci zuwa gidaje masu inganci, daga sufurin kayayyaki ta amfani da doki zuwa motoci, zaman rayuwar al’ummar Jino na samun kyautatuwa matuka. Na zauna a gida mai rataye da hoton marigayi Mao Zedong, ina dandana shayin Pu’er, ina ganin cewa, al’ummar Jino sun tabbatar da bunkasuwa cikin sauri karkashin manufar kawar da talauci da gwamnatin kasar Sin ta dauka. A halin yanzu kuma, al’ummar Jino na kokarin kama hanyar zamanintar da kan su. (Mai zane da rubuta: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7
Daga Birnin Sin

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Next Post
Bara-gurbin Ma’aikaci Da Hadarin Wargaza Bin Tsarin Cancanta

Bara-gurbin Ma’aikaci Da Hadarin Wargaza Bin Tsarin Cancanta

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version