Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Nda-Isaiah Ya Tafi Lokacin Da Aka Fi Bukatar Shi –Janar Abdulsalami

by Muhammad
December 16, 2020
in LABARAI
1 min read
Janar Abdulsalami
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Nasir S. Gwangwazo,

Tsohon Shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar, ya bayyana cewa, Shugaban jaridar LEADERSHIP kuma Kakakin Nupe, Marigayi Sam Nda-Isaiah, ya rasu a lokacin da a ka bukatar shi ne.
Janar Abdulsalami ya bayyana hakan ne a wasikar da ya aike wa iyalin mamacin, wanda ya rasu a ranar Juma’ar da ta gabata da daddare, ta hannun kanin marigayin, Mista Abraham Nda-Isaiah.
A cikin wasikar, wacce tsohon janar din ya santa wa hannu da kansa a jiya Talata, ya ce, “a madadin iyalina da ni kaina, Ina mai mika sakon ta’aziyyata cike da alhini da jimamin rasuwarsa a daidai lokacin da a ka fi bukatar shi.”
Tsohon Shugaban Kasar, bayan ya roki rahamar Allah ga mamacin, sai ya cigaba da cewa, “gibin da ya bari a cikin iyalinsa, jaridar LEADERSHIP da bangaren yada labarai bakidaya, ba zai taba cikuwa ba, amma mun amshi dangana saboda kasancewar zai riski Ubangijinsa ne. Kowane rai mamaci ne.”
Daga na sai Janar Abdulsalami ya kara da cewa, hakika rayuwar marigayin ta yi matukar tasiri ga mutanen da su ka yi aiki da shi a lokacin da ya ke raye. Daga nan sai ya yi fatan samun kyakkyawar rayuwa ga wadanda ya bari a baya.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Majalisa Ga Gwamnati: Ku Tabbatar Daliban Kankara Sun Dawo Lafiya Da Rai

Next Post

Tun Farko Sarki Sanusi Bai Cancanci Zama Sarkin Kano Ba, Inji Ganduje

RelatedPosts

Zaben Dan Majalisa

Za A yi Zaɓen Gwamnan Anambara Ranar 6 Ga Nuwamba – INEC

by Sulaiman Ibrahim
4 hours ago
0

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa a ranar...

Ogun

Fashewar Tankar Mai Ya Ci Rayuwar Mutum Uku Da Jittaka Shida A Ogun

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, A ranar Talata ne mutum uku...

Bafarawa

’Yan Nijeriya Sun Fi So A Magance Rashin Tsaro Fiye Da Korona, Cewar Bafarawa

by Muhammad
11 hours ago
0

A Juya Kuɗin Rigakafin Cutar Naira Biliyan 400 Zuwa Tsaro...

Next Post
Sarki Sanusi

Tun Farko Sarki Sanusi Bai Cancanci Zama Sarkin Kano Ba, Inji Ganduje

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version