Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

NDE Ta Ƙaddamar Da Taron Haɓaka Aikin Yi Ga Matasa 18,000 A Kebbi

by Tayo Adelaja
October 27, 2017
in RAHOTANNI
4 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin Kebbi

Hukumar NDE ta ƙasa ta ƙaddamar da taron bukin haɓaka aikin yi da kuma  horas da matasa 18,000 a Jihar Kebbi kan sana’o’in zamani iri daban-daban tsakanin mata da maza duk faɗin  jihar ta Kebbi.

Taron ya gudana ne a ɗaukin taro na kwalejin Waziri Umaru da ke Birnin-kebbi a shekaran jiya. Wanda bukin horaswar ya samu halartar manyan shugabanin gwamnatin tarayya da ta jihar kamar ministan kwadago da Aiki Sanata Chris Nwabueze Ngige, Shugaban hukumar Samar da Aikin yi ta ƙasa dakta  Nasir Ladan Muhammad Argungu,Mataikin Gwamnan jihar kebbi Alhaji Samaila Yombe Dabai, mataikin shugaban kwamitin kwadago da Samar da aikin yi a majalisar dokoki dakta  Manir Baba Dan Agunde, Sanata Muhammad Adamu Aliero.

Sauran sun hada Gwamnan jihar kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu, Sarkin Gwandu Alhaji Muhammad Iliyasu Bashar, Sarkin Kabin Argungu Alhaji Samaila Muhammad Mera, Kakakin majalisar dokoki ta jihar kebbi Alhaji Samaila Abdulmuminu Kamba da kuma wakilin ƙaramin ministan kwadago da Aiki .

Har ila yau ministan ya ci gaba da cewa ya yi farin cikin gabatar da jawabi mai mahimmanci a wannan muhimmin  taro, na ƙaddamar da horo da horos da kuma karfafawa  matasa fiye da 18,000 da hukumar NDE shirya, wanda shine kokarin da za a iya domin biyan bukatun matasa  marasa aikin yi ga ‘yan ƙaunatattunmu, musamman ma matasa, don samun damar yin aiki wanda  zasu iya dogarowa ga  Kansu.

sai dai ya ce shugaban Muhammadu Buhari a kwanan nan, shugaban ya nuna kyakkyawar fatawa ta karfafa matasa ta hanyar tsarin fasaha da kuma tallafawa hukumomin tarayya da ke da nauyin kundin tsarin mulki.

Hakazalika ministan ya nuna jidadin sa kan irin  yadda gwamnatin jihar kebbi ke  bada goyun bayan ta wurin ganin an Samar wa  matasa aikin yi a ƙasar nan.

Daga nan kuma ya ce ya kamata a lura da cewa jihar Kebbi ta sami albarka ga amfamin  noma a cikin bangarori masu mahimmanci da kuma ma’adinai wanda ke iya samar da zuba jarurruka da hannun kokarin  Gwamna Bagudu wanda ya jagoranci kokarin na yin amfani da wannan damar don ci yarda  jihar kebbi da ma ƙasar Nijeriya a gaba ta hanyoyin noma.

Shima da yake  nasa jawabi Shugaban hukumar NDE  ta ƙasar dakta  Nasir  Ladan Muhammad Argungu, ya bayyana cewa, manyan  baki  maza da  mata da ke wannan wurin , mun taru a yau don ƙaddamar da horo da horassu wa ta fiye da 18,000 har yanzu marasa  aikin yi a cikin rayuwa mai mahimmanci da ma’ana. Za a horar da daruruwan mutane dubu huɗu da ɗari takwas da ashirin (4820) a fannoni daban-daban da suka shafi fasahar gargajiya domin dogaro da Kansu.

Shugaban hukumar ta NDE ya ci gaba da cewa horas suwar ta kunshi fanoni uku ne, wanda  horas suwar zata  kai kimanin  mako biyu ana gudanar da ita   ,  horas suwar ta hada da   ilimin  kiyon  dabbobin da al’umma ke da amfani da su a cikin ƙasar mu Nijeriya. Horas da  manoma ilimin yadda zasu  jagoranci  haɗin kai tare da ci gaba da hulda   da bankunan kudi ta hanyar noma. A nan za a ba wa ‘yan makaranta kwaskwarima a kan hankali da tunani don sauya aikin yin  aikin gona kamar yadda ya dace da aikin da aka biya.

Sauran sun hada da  kashe waɗanda suka shiga za su zama ainihi a cikin gari don rage haɗarin samar da abinci a kasuwa.

Shima da yake  gabatar da jawabin sa a wurin taron  Gwamnan jihar kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya bayyana jindadin sa kan wannan shirin da hukumar NDE ta kawo a jihar kebbi, inda ya yabawa  gwamnatin tarayya da kuma shugabanin hukumar ta NDE kan soma ƙaddamar da shirin da matasan jihar kebbi.

Gwamnan Bagudu ya ce  “ gwamnatin jihar kebbi zata  bada goyon baya ga  shirin horas da matasan jihar kebbi sana’o’i hannu na zamani domin su iya dogaro da kawunan su”. Ya ci gaba da cewa” zamu bada tallafin kudi ga  shirin Samar da aikin yi ga  matasan jihar kebbi kai har  da ƙasa baki ɗaya.

Hakazalika Gwamna Bagudu ya yi kira ga  matasan jihar ta kebbi da su sadaukar da Kansu wurin ganin cewa su koyi abin da ake son su iya a lokacin karɓar horas suwar, domin samun nasarar abin da suka koya.

Daga nan yana godiya ga duk manyan bakin na gida dana wajen jihar da suka halarci taron  bukin  ƙaddamar da horas suwar ta matasa domin Samar musu da aikin yi a cikin jihar ta kebbi da kuma ƙasar Nijeriya baki ɗaya.

SendShareTweetShare
Previous Post

MUƘALA: Hattara Dai Inyamurai (5)

Next Post

Shata Ya Tafi, Shata Ya Dawo

RelatedPosts

ACF

Kungiyar ACF Da Badakalar Jagoranci A Yankin Arewa

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Zailani Bappa, Al’ummar Arewa da dama za su tabbatar...

NLC

Mafi Karancin Albashi: Wata Kungiya Ta Yi Tir Da Kalaman NLC Akan Dan Majalisa Datti Babawo

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Bello Hamza, Wata kungiya mai zaman kanta mai suna...

Abduljabbar

Abduljabbar Bai Kai Darajar A Yi Masa Gangami Ba –Sheikh Khalil

by Muhammad
3 days ago
0

Ya Ce, Dalilin Da Ya Sa Sarkin Musulmi Ya Hana...

Next Post

Shata Ya Tafi, Shata Ya Dawo

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version