Idris Aliyu Daudawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutum 43 Masu Safara Miyagun Kwayoyi A Kano

by Idris Aliyu Daudawa
January 31, 2021
in LABARAI
2 min read
NDLEA Ta Kama Mutum 43 Masu Safara Miyagun Kwayoyi A Kano
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar yaki da fataucin muggan kwayoyi ta kasa (NDLEA)ta reshen jihar Kano ta bayyana cewar ta kame wasu mutane 43 da ake zargi da fataucin muggan kwayoyi a cikin watan Janairu da muke ciki.
Dokta Ibrahim Abdul wanda Kwamandan NDLEA na jihar, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake wata tattaunawa da manema labarai ranar Juma’a a Kano.
Abdul ya ce an kama su wadanda ake zargin a wurare daban-daban a cikin jihar, wannan kuma ya biyo bayan gudanar da wani babban samame da jami’an rundunar suka yi.
Ya bayyana cewar a lokacin da suke gudanar da ayyukansu daban-daban, rundunar ta samu nasarar cafke kilogram 581.702 na wasu daga abubuwan da aka haramta daban-daban a fadin jihar ta Kano.
Ya kara da war “A cikin watan Janairu da muke da muke ciki, mun sami nasarar cafke kilogiram 533.553 na wiwi, kilogiram 48.052 na Psychotropic da kuma kilogiram 0.097 na hodar iblis kamar dai yadda ya bayyana”.
Abdul ya kara da cewar a tsakanin wannan lokaci, rundunar ta samu nasarar yanke hukunci a kan wasu mutane hudu da ake zargi a Babbar Kotun Tarayya da ke Kano.
“A lokacin da ake ciki an tura masu amfani da kwayoyi 76 wadnada aka kai su wurin da zaa rika basu (shawara), sai kuma wasu mutane hudu wadanda aka riga aka saba dasu,saboda yau da kullun, bugu da kari kuma an salami mutane biyu bayan da aka kammala basu shawarar data kamata.
Daga karshe Abdul yace an samu ita nasarar ne sakamakon namijin kokarin da su jami’an na NDLEA suka yi da kuma goyon bayan masu ruwa da tsaki daban-daban akan shi al’amarin na yaki da shan muggan kwayoyi.
Ya yaba wa Shugaba Muhammadu Buhari akan nadin da yayi wa Birgediya-Janar mai ritaya. Muhammed Buba Marwa a matsayin sabon Shugaban hukumar ta NDLEA, ya kuma kara da cewar ba a dade da fara aikin shi sabon shugaban ba, har kwalliya ta fara biyan kudin sabulu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Maslaha, Fahimtar Juna Ne Kadai Za Su Kawo Ci Gaban kungiyar Manoma Gyada- Aimu Foni

Next Post

Zaben Kananan Hukumomin Kano, Abin Kunya Aka Jawo Wa APC – Sharada

RelatedPosts

Alkalin Kotun Koli, Ngwuta, Ya Rasu A Abuja

Alkalin Kotun Koli, Ngwuta, Ya Rasu A Abuja

by Idris Aliyu Daudawa
12 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Mai Shari’a Sylvester Ngwuta, alkalin kotun koli...

Tinubu Ya Bukaci Matasa Su Nisanci Bangar Siyasa

by Idris Aliyu Daudawa
19 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Jagoran jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya...

E Call

Shirin Kula Da Zirga-zirgar Manyan Motoci Na ‘E-Call’ Zai Kawo Karshen Cunkoso A Tashar Jiragen Ruwan Nijeriya -Hadiza Bala Usman

by Idris Aliyu Daudawa
19 hours ago
0

By Bello Hamza, An tabbatar wa masu hulda da tashoshin...

Next Post
Zaben Kananan Hukumomin Kano, Abin Kunya Aka Jawo Wa APC – Sharada

Zaben Kananan Hukumomin Kano, Abin Kunya Aka Jawo Wa APC - Sharada

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version