Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NECO Za Ta Binciki Zargin Magudin Jarrabawar Wata Cibiya A Kaduna

by Khalid Idris Doya
December 9, 2020
in LABARAI
2 min read
NECO
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar gudanarwa na hukumar shirya jarrabawar kammala sakandari ta Nijeriya (NECO) ta kaddamar da wani kwamiti mai karfi, wanda zai binciki zarge-zargen magudin jarrabawa da a ke yi kan wasu jami’anta da wata cibiyar zana jarrabawa tare da wasu daliban da su ka zana jarrabarwar kan batun satar amsa da magudin jarrabawa a bisa wani rahoton da wata kafa ta bankadowa.

Kafar talabijin ta Signature ta sake tare da fitar da wani faifan bidiyon da ta dauka a boye da ke nuna yadda a ke karya dokar gudanar da jarrabawa da tafka magudi a daya daga cikin cibiyoyin zana jarrabawar ta Fabian Kings and Kueens International School da ke Kabala ta yamma, a jihar Kaduna da ke da lambar zana jarrabawa ‘0140721’ da ke nuna yadda aka tafka magudin jarrabawa a yayin zana jarrabawar da aka kammala a baya-bayan nan na ‘2020 SSCE’.

samndaads

A sanarwar manema labarai da jami’in yada labarai na NECO, Azeez Sani ya fitar, ya ce, sun gano makarantar da bidiyon ke nunawa tare da daukan matakan da suka dace kan batun.

A cewar sanarwar: “A bisa matsayar NECO na cewa ba za ta taba lamuntar kowani irin magudi da satar jarrabawa ba, cikin gaggawa ta dauki matakin hanzari kan cibiyar da aka gano tare da killace daliban gami da bincike kan takardun jarrabawar da suka zana,” a cewar Sani.

Ya ce, muddin aka tabbatar da abun da ake zargi to za su dauki matakin soke dukkanin jarrabawar da aka zana a wannan cibiyar nan take, “Dukkanin sakamakon jarawabar za a sokesu da zarar aka tabbatar da wannan zargin, sannan, makarantar za a daina kula da ita, su kuma jami’an da suke da hannu a lamarin za a gurfanar da su kamar yadda ke kunshe cikin sashin dokar zabe 33 na shekarar 1999,”

“Daga bisani, Hukumar NECO ta yaba da kokarin hukumar gudanarwa na gidan talebijin din Signature a bisa himmarsu na tsarkake badalaka a harkar jarrabawa, mu na rokon da fatan masu ruwa da tsaki za su yi koyi da hakan,” inji sanarwar ta NECO.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Bauchi Ta Ware Biliyan N213 A Matsayin Kasafin 2021

Next Post

Malaman Firamare Ba Su Karbar Albashin N18,000 A Kananan Hukumomin Borno – NUT

RelatedPosts

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

by Khalid Idris Doya
3 hours ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) da...

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

by Khalid Idris Doya
9 hours ago
0

Gwamna jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal Ya sanar da Mutuwar...

Sakatariyar

Sakatariyar Karamar Hukumar Da Ake Wata Guda Ba A Shige Ta Ba A Kano

by Khalid Idris Doya
17 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kananan Hukumomi ne ke zaman gimshikai...

Next Post
NUT

Malaman Firamare Ba Su Karbar Albashin N18,000 A Kananan Hukumomin Borno – NUT

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version