Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Nijeriya Da Masu Zuba Jari Daga Waje Sun Cimma Yarjejeniyar Hakar Zinari

by Muhammad
December 1, 2020
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Zinari
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Yusuf Shuaibu

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta rattaba hannu a yarjejeniya da masu zuba jari na kasashen ketare, domin zuba jari hakar zinarin Nijeriya. An bayyana cewa, gwamnatin tarayyar ta rattaba hannu ne da kamfanin bunkasa zinari da ke kasar Egypt, an dai cimma wannan yarjejeniyar ne tare da ma’aikatar ma’adanar da bunkasa karafuna  domin zuba jari a bangaren zinarin Nijeriya.

samndaads

Da yake jawabi a wajen cimma yarjejeniyar, karamin ministan ma’aikatan ma’adanar da bunkasa karafuna, Uchechukwu Ogah ya bayyana cewa, yarjejeniyar da aka cimma da kamfanin La Mancha na kasar Egypt, kokari ne na  babban janyo hankalin masu zuba jari wanda sai bayar da sakamako mai matukar mahimmanci.

Kamfanin Egyptian African Arab Company for Debelopment da ke Cairo a kasar Egypt ne ya shirya wannan yarjejeniya.

Ogah ya ce, “burin mu dai shi ne mu janyo hankalin masu zuba jari na kasashen ketare ta yadda za su zuba kudadensu a bangaren hakar ma’adananmu ta hanyar samarwa da sarrafawa a Nijeriya.”

Shugaban gamayyar kamfanonin La Mancha, Naguib Sawiris, ya bayyana cewa, kundin rattaba yarjejeniyar na kamfanin ya fara aiki ne tun da dadewa a Nijeriya. Ya kara da cewa, La Mancha sun dade suna neman  irin wannan damar wanda za su zuba jari a bangaren hakar ma’adanai a fadin Afirka. Ya ce, Nijeriya tana da ishasshen zinari wanda za a zuba jari. Ya ce, kamfanin  zai fara gudanar da aiki ne a farkon shekarar 2021.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Bankin CDB Na Kasar Sin Ya Samar Da Rance Don Taimakawa Shirin Kawar Da Talauci

Next Post

Mura Cutar Dan Gata

RelatedPosts

Kangin Talauci

Shirin Tsamo Mutane Miliyan Biyu Daga Kangin Talauci Ya Kankama – Osinbajo

by Muhammad
3 days ago
0

Bayan samun nasarar kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki...

Talakawan Nijeriya

Talakawan Nijeriya Miliyan 24.3 Sun Samu Tallafin Naira 5,000 Kowanne – Ministar Jinkai

by Muhammad
3 days ago
0

A ranar Talata ne, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, sama...

FIRS

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS) ta bayyana cewa, ta...

Next Post
Mura

Mura Cutar Dan Gata

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version